• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kirsimeti

Yayin da Kiristocin Jihar Gombe ke bin sahun takwarorinsu na duniya wajen gudanar da bukukuwan Kirsimeti na bana, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukace su da dabbaka dabi’un kauna, sadaukarwa da kuma hakuri kamar yadda koyarwa Yesu Almasihu ya horar da su.

A sakonsa na taya murna dauke da sanya hannun Ismaila Uba Misilli, babban daraktan yada labara gwamnan, ya bukaci mabiya addinin Kirista a jihar da ma daukacin al’ummar Nijeriya baki daya da su ci gaba da karfafa imaninsu da Allah, tare da tabbatar da zaman lafiya da hadin kai.

  • Adadin Kudin Da Kowacce Kasa Ta Samu A Gasar Cin Kofin Duniya
  • Shugaban Kasar Equatorial Guinea: Kasashen Yamma Sun Yayata Furucin Wai “Sin Na Kafa Tarkon Bashi” A Yunkurin Su Na Dakile Kasar

Ya kuma bukaci jama’a su sake sadaukar da kan su ga addu’o’i, abin da ya ce yana da matukar tasiri ga zaman lafiya da hadin kan al’umma.

Gwamnan ya bayyana cewa “A wannan muhimmin biki na Kirsimeti, ina mika sakon fatan alheri ga al’ummar Kirista da daukacin al’ummar kasar nan.

“Wannan lokacin yana tunatar da mu bukatar dabbaka kyawawan halaye na kauna, sadaukarwa da kuma hakuri.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

“Ina kira a gare mu duka, mu yi tunani a kan darusan wannan lokaci ke koyarwa da suka hada da kauna da soyayya da kuma kyauta.”

Da ya ke tabbatar da aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bullo da tsare-tsare da manufofin da za su inganta hadin kai da zaman lafiya a jihar.

Gwamnan ya bukaci jama’ar jihar su yi amfani da wannan lokacin wajen yi wa jihar da kasa addu’ar zaman lafiya da ci gaba don gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali.

“Ina kira a gare ku, ku yi amfani da wannan lokaci wajen sadaukar da kai cikin addu’o’i ga Allah Madaukakin Sarki don ya dawo mana da zaman lafiya a cikin al’ummarmu, mu yi addu’ar Allah Ya dawo mana da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar kar su yanke kauna, su ci gaba da kasancewa da bege duk da irin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da duniya ke ciki, wadda cutar Korona da yakin Rasha da Ukraine da kuma rashin tsaro da ake fama da shi a Nijeriya suka haifar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.