• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Kiristocin Jihar Gombe ke bin sahun takwarorinsu na duniya wajen gudanar da bukukuwan Kirsimeti na bana, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukace su da dabbaka dabi’un kauna, sadaukarwa da kuma hakuri kamar yadda koyarwa Yesu Almasihu ya horar da su.

A sakonsa na taya murna dauke da sanya hannun Ismaila Uba Misilli, babban daraktan yada labara gwamnan, ya bukaci mabiya addinin Kirista a jihar da ma daukacin al’ummar Nijeriya baki daya da su ci gaba da karfafa imaninsu da Allah, tare da tabbatar da zaman lafiya da hadin kai.

  • Adadin Kudin Da Kowacce Kasa Ta Samu A Gasar Cin Kofin Duniya
  • Shugaban Kasar Equatorial Guinea: Kasashen Yamma Sun Yayata Furucin Wai “Sin Na Kafa Tarkon Bashi” A Yunkurin Su Na Dakile Kasar

Ya kuma bukaci jama’a su sake sadaukar da kan su ga addu’o’i, abin da ya ce yana da matukar tasiri ga zaman lafiya da hadin kan al’umma.

Gwamnan ya bayyana cewa “A wannan muhimmin biki na Kirsimeti, ina mika sakon fatan alheri ga al’ummar Kirista da daukacin al’ummar kasar nan.

“Wannan lokacin yana tunatar da mu bukatar dabbaka kyawawan halaye na kauna, sadaukarwa da kuma hakuri.

Labarai Masu Nasaba

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

“Ina kira a gare mu duka, mu yi tunani a kan darusan wannan lokaci ke koyarwa da suka hada da kauna da soyayya da kuma kyauta.”

Da ya ke tabbatar da aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bullo da tsare-tsare da manufofin da za su inganta hadin kai da zaman lafiya a jihar.

Gwamnan ya bukaci jama’ar jihar su yi amfani da wannan lokacin wajen yi wa jihar da kasa addu’ar zaman lafiya da ci gaba don gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali.

“Ina kira a gare ku, ku yi amfani da wannan lokaci wajen sadaukar da kai cikin addu’o’i ga Allah Madaukakin Sarki don ya dawo mana da zaman lafiya a cikin al’ummarmu, mu yi addu’ar Allah Ya dawo mana da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar kar su yanke kauna, su ci gaba da kasancewa da bege duk da irin kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da duniya ke ciki, wadda cutar Korona da yakin Rasha da Ukraine da kuma rashin tsaro da ake fama da shi a Nijeriya suka haifar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeInuwa YahayaKiristociKirsimeti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Kudin Da Kowacce Kasa Ta Samu A Gasar Cin Kofin Duniya

Next Post

Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

Related

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Labarai

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

55 seconds ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

11 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

12 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

12 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

13 hours ago
Next Post
Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

Tsare-tsare Na Zahiri Da Za Su Matso Da Mutane Kusa Da Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.