ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adadin Kudin Da Kowacce Kasa Ta Samu A Gasar Cin Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Khalifa International Stadium at Gulf Cup in Riyadh. 2022 FIFA World Cup Qatar

Khalifa International Stadium at Gulf Cup in Riyadh. 2022 FIFA World Cup Qatar

Bayan kammala gasar cin kofin duniya a yammacin ranar Lahadi wanda Argentina ta doke kasar Faransa, hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) ta sanar da adadin kudaden da kowacce kasa ta samu tun daga wasannin cikin rukuni har zuwa wasan karshe.

 Hakan na nufin baya ga kofin duniya da sarkar zinari da aka bai wa ‘yan wasa, Argentina za ta bar Katar da miliyoyin daloli saboda a bana hukumar kwallon kafa ta duniya ta ware kudin da za a ci kyauta da yawansu ya kai dala miliyan 440.

  • Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu
  • Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka: Gudummawar Kamfanonin Sin A Fannin Raya Hulda Da Kasashen Afirka

Kasashe 32 daga fadin duniya da suka wakilci nahiyoyinsu za su bar Katar da akalla dala miliyan tara kowannensu.

ADVERTISEMENT

Tuni FIFA ta fitar da abin da kowacce kasa za ta samu gwargwadon matakin da ta kai a gasar da kuma sauran kasashen da suka samu damar zuwa gasar amma suka gaza tsallake matakin rukuni za su koma gida ne da dala miliyan tara kowannensu.

 Hakan na nufin kasashen Katar da Ecuador da Wales da Iran da Medico da Saudi Arabia da Denmark da Tunisia da Kanada da Belgium da Germany da Costa Rica da Serbia da Kamaru da Ghana da da kuma Uruguay sun samu dala miliyan tara kowannensu.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Sai kuma kasashen da suka samu kai wa zagayen ‘yan 16, amma gudunsu ya kare daga nan da suka hada da Amurka da Senegal da Australia da Poland da Sifaniya da Japan da Switzerland da kuma Koriya ta Kudu, kowannensu ya samu dala miliyan 13.

 Sannan wadanda suka samu kansu a zagayen kuarter-finals da suka hada da Brazil da Netherlands da Portugal da kuma England sun samu dala miliyan 17 kowannensu kamar yadda FIFA ta bayyana.

A fagen neman na uku kuwa, ma’ana gurbin da Maroko da Croatia suka samu kansu bayan kai wa zagayen kusa da karshe, Croatia ta samu dala miliyan 27, yayin da Maroko ta koma gida da dala miliyan 25 a matsayin na hudu.

Sai kuma zagayen karshe da aka warewa dala miliyan 72, Faransa da ta yi rashin nasara ita ce mai dala miliyan 30, yayin da Argentina da ta lashe kofi za ta koma gida da dala miliyan 42.

 Har ila yau, FIFA ta kara yawan kudin da za a ci idan aka kwatanta da wasannin baya da dala miliyan 40, domin a shekarar 2018 kasashen da suka samu halartar gasar sun raba dala miliyan 400 ne.

 Kafin 2006 kasashen da suka lashe gasar kofin duniya ba su taba wuce karbar sama da dala miliyan 10 ba, sannan Italiya ma da ta lashe kofin duniya a shekarar 1982 dala miliyan 2.2 kawai ta samu.

Ta ina Kudaden Suke Fitowa?

Tambayar cewa a ina hukumar kwallon kafa ke samun kudade tana da saukin amsawa, ta hanyar shirya gasa domin a gasar kofin duniya ta 2018 kawai, FIFA ta samu sama da dala biliyan 4.6 na kudin shiga.

 Kuma kusan duk shekara hukumar ba ta rasa wata gasa da za ta shirya, duk da ba lalle ta samu makudan kudade ba kamar a gasar kofin duniya ta maza ba, sai dai a shekarar 2021 ne ma da ba ta shirya gasa ba, amma duk da haka sai da FIFA ta samu dala miliyan 766.

 Mafi yawan ribar da FIFA ke samu na fitowa ne ta hanyar kudaden da ake biyanta wajen samun damar nuna wasannin kofin duniya da sauran gasa daban-daban da take shiryawa kuma gasar kofin duniya ce gasar da aka fi kallo a duk duniya, inda aka yi hasashen biliyoyi sun kalli gasar Katar 2022.

 A gasar kofin duniya ta wadda Rasha ta karbi bakunci, sama da mutum biliyan hudu ne suka kalli wasan ta talabijin da sauran kafofin sadarwa na zamani. Haka kuma FIFA na karbar makudan kudade ga kamfanoni da ke tallar hajojinsu a lokacin da gasa ke gudana.

 Tun kafin fara gasar cin kofin duniya na 2018, FIFA ta samu kusan dala biliyan biyu daga kamfanonin da ke son FIFA ta yi musu talla a gasar, sannan wasu kamfanoni kamar na gyam na bidiyo da ya shafi kwallon kafa na biyan FIFA makudan kudade domin amfani da sunanta, kuma kamfanin gyam din bidiyo na EASPORTS da ke Amurka ya bai wa FIFA dala biliyan 20 don amfani da sunanta a tsawon shekaru 20.

 Wata hanyar kuma da FIFA ke samun kudin shiga ita ce sayar da tikitin shiga kallon wasanni, domin kusan tikiti miliyan uku FIFA ta sayar ga wadanda ke son kallon gasar Katar 2022 da aka kammala kuma farashin tikitin na farawa ne daga dala 100 zuwa dala 1,100.

Saboda haka ko a tikiti kawai FIFA na samun biliyoyin daloli na kudin shiga.

Kofin Duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.