ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adadin Kudin Da Kowacce Kasa Ta Samu A Gasar Cin Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Khalifa International Stadium at Gulf Cup in Riyadh. 2022 FIFA World Cup Qatar

Khalifa International Stadium at Gulf Cup in Riyadh. 2022 FIFA World Cup Qatar

Bayan kammala gasar cin kofin duniya a yammacin ranar Lahadi wanda Argentina ta doke kasar Faransa, hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) ta sanar da adadin kudaden da kowacce kasa ta samu tun daga wasannin cikin rukuni har zuwa wasan karshe.

 Hakan na nufin baya ga kofin duniya da sarkar zinari da aka bai wa ‘yan wasa, Argentina za ta bar Katar da miliyoyin daloli saboda a bana hukumar kwallon kafa ta duniya ta ware kudin da za a ci kyauta da yawansu ya kai dala miliyan 440.

  • Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu
  • Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka: Gudummawar Kamfanonin Sin A Fannin Raya Hulda Da Kasashen Afirka

Kasashe 32 daga fadin duniya da suka wakilci nahiyoyinsu za su bar Katar da akalla dala miliyan tara kowannensu.

ADVERTISEMENT

Tuni FIFA ta fitar da abin da kowacce kasa za ta samu gwargwadon matakin da ta kai a gasar da kuma sauran kasashen da suka samu damar zuwa gasar amma suka gaza tsallake matakin rukuni za su koma gida ne da dala miliyan tara kowannensu.

 Hakan na nufin kasashen Katar da Ecuador da Wales da Iran da Medico da Saudi Arabia da Denmark da Tunisia da Kanada da Belgium da Germany da Costa Rica da Serbia da Kamaru da Ghana da da kuma Uruguay sun samu dala miliyan tara kowannensu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Sai kuma kasashen da suka samu kai wa zagayen ‘yan 16, amma gudunsu ya kare daga nan da suka hada da Amurka da Senegal da Australia da Poland da Sifaniya da Japan da Switzerland da kuma Koriya ta Kudu, kowannensu ya samu dala miliyan 13.

 Sannan wadanda suka samu kansu a zagayen kuarter-finals da suka hada da Brazil da Netherlands da Portugal da kuma England sun samu dala miliyan 17 kowannensu kamar yadda FIFA ta bayyana.

A fagen neman na uku kuwa, ma’ana gurbin da Maroko da Croatia suka samu kansu bayan kai wa zagayen kusa da karshe, Croatia ta samu dala miliyan 27, yayin da Maroko ta koma gida da dala miliyan 25 a matsayin na hudu.

Sai kuma zagayen karshe da aka warewa dala miliyan 72, Faransa da ta yi rashin nasara ita ce mai dala miliyan 30, yayin da Argentina da ta lashe kofi za ta koma gida da dala miliyan 42.

 Har ila yau, FIFA ta kara yawan kudin da za a ci idan aka kwatanta da wasannin baya da dala miliyan 40, domin a shekarar 2018 kasashen da suka samu halartar gasar sun raba dala miliyan 400 ne.

 Kafin 2006 kasashen da suka lashe gasar kofin duniya ba su taba wuce karbar sama da dala miliyan 10 ba, sannan Italiya ma da ta lashe kofin duniya a shekarar 1982 dala miliyan 2.2 kawai ta samu.

Ta ina Kudaden Suke Fitowa?

Tambayar cewa a ina hukumar kwallon kafa ke samun kudade tana da saukin amsawa, ta hanyar shirya gasa domin a gasar kofin duniya ta 2018 kawai, FIFA ta samu sama da dala biliyan 4.6 na kudin shiga.

 Kuma kusan duk shekara hukumar ba ta rasa wata gasa da za ta shirya, duk da ba lalle ta samu makudan kudade ba kamar a gasar kofin duniya ta maza ba, sai dai a shekarar 2021 ne ma da ba ta shirya gasa ba, amma duk da haka sai da FIFA ta samu dala miliyan 766.

 Mafi yawan ribar da FIFA ke samu na fitowa ne ta hanyar kudaden da ake biyanta wajen samun damar nuna wasannin kofin duniya da sauran gasa daban-daban da take shiryawa kuma gasar kofin duniya ce gasar da aka fi kallo a duk duniya, inda aka yi hasashen biliyoyi sun kalli gasar Katar 2022.

 A gasar kofin duniya ta wadda Rasha ta karbi bakunci, sama da mutum biliyan hudu ne suka kalli wasan ta talabijin da sauran kafofin sadarwa na zamani. Haka kuma FIFA na karbar makudan kudade ga kamfanoni da ke tallar hajojinsu a lokacin da gasa ke gudana.

 Tun kafin fara gasar cin kofin duniya na 2018, FIFA ta samu kusan dala biliyan biyu daga kamfanonin da ke son FIFA ta yi musu talla a gasar, sannan wasu kamfanoni kamar na gyam na bidiyo da ya shafi kwallon kafa na biyan FIFA makudan kudade domin amfani da sunanta, kuma kamfanin gyam din bidiyo na EASPORTS da ke Amurka ya bai wa FIFA dala biliyan 20 don amfani da sunanta a tsawon shekaru 20.

 Wata hanyar kuma da FIFA ke samun kudin shiga ita ce sayar da tikitin shiga kallon wasanni, domin kusan tikiti miliyan uku FIFA ta sayar ga wadanda ke son kallon gasar Katar 2022 da aka kammala kuma farashin tikitin na farawa ne daga dala 100 zuwa dala 1,100.

Saboda haka ko a tikiti kawai FIFA na samun biliyoyin daloli na kudin shiga.

Kofin Duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

Gwamna Gombe Ya Taya Kiristoci Murnar Kirsimeti, Ya Hore Su Kan Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.