ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Karɓo Sakamakon Jarabawar WAEC Da Hukumar Ta Riƙe

by Sulaiman
2 years ago
Gwamna Lawal

A ƙoƙarin da ya ke yi don ganin ya cika alƙawuran da ya yi wa Zamfarawa, musamman a harkar ilimi, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu nasarar karɓo sakamakon jarabawar WAEC na ‘yan asalin jihar, wanda Hukumar ta ƙi saki saboda rashin biyan kuɗin jarabawar.

Ita dai Hukumar da ke kula da shirya jarabawar ta WAEC ta riƙe sakamakon jarabawar ɗaliban jihar Zamfarar ne sakamakon bashin Naira Biliyan 1.4 da ta ke bin gwamnatocin jihar da suka gabata.

  • Zannan Bungudu Ya Gina Masallatai 20 Makarantun Islamiyya 15 A Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin ‘Pulaku’ Don Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawu Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Gwamnan ya samu ganawa da shugabannin Hukumar ne a ofishin sa da ke Abuja ranar Litinin da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a ziyarar da suka kawo wa Gwamnan, sun samu ganawa da shugabannin Hukumar bisa jagorancin shugabar sashen mulki da harkokin kuɗi, Hajiya Binta Abdulkadir da kuma shugaban ofishin WAEC, Dr. Amos J. Dangut.

Ya ci gaba cewa, “A ƙoƙarin da gwamnatin nan ke yi na ganin ta haƙƙaƙa shirin ta na sanya dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, Gwamna Dauda Lawal ya karɓi baƙuncin Shugabannin Hukumar WAEC a ofishin sa da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

“Gwamnan, wanda ke tare da Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, sun tattauna da shugabbanin Hukumar ta WAEC a kan abin da ya shafi basussukan da ake bin jihar Zamfara na gwamnatocin da suka gabata.

“Rashin biyan waɗannan kuɗaɗe na tsawon shekaru ya sa hukumar ta ƙi bayyana sakamakon jarabawar ɗaliban jihar suka zana, wanda wannan yanayi ya jawo wa ɗaliban da suka kammala Jami’o’i rashin zuwa yi wa ƙasa hidima na NYSC saboda rashin sakamakon na WAEC a hannun su.

Sanarwar ta Idris ta ƙara da bayyana cewa, a wancan zaman, an cimma matsaya tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Hukumar ta WAEC kan yadda za a shawo kan lamarin bashin.

“A ƙarshen zaman, Hukumar ta amince za ta fitar da sakamakon jarabawar da suka gabata, tare da amincewa ɗaliban jihar za su zauna don zana jarabawar WAEC ta shekarar 2024.

“Duk ɓangarorin byu sun amince da tsarin da aka yi na biyan bashin da ake bi, tare da cewa za a saki sakamakon jarabawar kafin ƙarshen watannan.”

A wannan ganawa dai, akwai manyan ma’aikatan Hukumar, waɗanda suka haɗa da Mr Ambrose Okelezo, shugaban shiyya; Mr Victor C. Odu, Daraktan kuɗi; da Mr Segun U. Jerumeh, Mataimakin Darakta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Tinubu Ya Isa Birnin New York Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya A Karo Na Farko

Tinubu Zai Halarci Taron AU Karo Na 37 A Birnin Addis Ababa Na Kasar Habasha

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.