Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya sanar da cewa, Gwamnatinsa za ta gina wani babban filin wasan kwallon guragu na zamani a jihar domin ganin Jihar ta yi kafada-da-kafada da takwarorinta a Nijeriya.
Ya ce, za a mika filin wasan ne ga shugabanni masu kula da masu bukata ta musamman a jihar.
- Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
- ‘Yansanda Sun Tsare Habashawa 24 A Dajin Kenya
Gwamnan ya bayyana hakan ne a wasan karshe na lashe gasar kofin kwallon ta guragu da kungiyar kwallon ‘Para Soccer’ ta Kebbi ta shirya, inda kungiyar Jega Para ta lallasa kungiyar Kebbi para da ci 3-0 a filin wasa na Haliru Abdu da ke Birnin Kebbi.
A cewar Gwamnan, filin wasan zai kasance daya daga cikin mafi inganci a yankin Arewacin kasar nan domin bunkasa harkokin wasanni a jihar Kebbi.
Gwamna Nasir ya bayyana jin dadinsa da yadda ‘yan wasan ke buga kwallon, Inda yace, wasannin akwai Nishadantrawa sosai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp