Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya rushe Majalisar Zartarwar Jihar tare da sauke Sakataren Gwamnatinsa, Barista Muhammed Ubandoma-Aliyu.
Gwamnan ya sanar da hakan a wani taron gaggawa da aka gudanar a daren Juma’a, bayan tafiyar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya kai ziyara ta kwana ɗaya jihar.
- Sin Za Ta Ji Ra’ayoyin Jama’a Kan Takardar Sunayen Kayayyakin Da Za Ta Kayyade Fitarwa Kasashen Waje
- Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025
Duk da cewa ba a bayyana dalilin wannan mataki ba, ana ta raɗe-raɗin sake fasalin majalisar saboda zargin rashin ɗa’a daga wasu mambobin majalisar.
Mutane sun kasa kunnuwa domin dalilin da ya sa gwamnan ya É—auki wannan mataki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp