• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
in Rahotonni
0
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Umar Namadi, FCA wanda Jaridar LEADERSHIP ta karrama shi a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2024, hakika ya nuna kwarewa duba da irin rawar da ya taka tun bayan da ya karbi ragamar jagorancin jihar a shekarar 2023.

Salon shugabancinsa irin wanda ba a saba ganinsa ba wajen samar da romon dimokradiyya ga jihar a kowane fanni ya cancanci a yaba masa.

  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Cambodia
  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde

Bayan rantsar da shi a shekarar 2023 nan take ya aiwatar da kyawawan manufofi da azamar sauya wa jihar fasali ta fuskar karfafa wa matasa da mata, ta fannin inganta Ilimi, lafiya, Noma, da ababen more rayuwa na bukatu da dama da saka baza a sassan jihar domin kowa ya amfana.

Daya daga cikin wadannan manufofi na kawo sauyi da ya aiwatar kasa da watanni uku da shigarsa ofis sun hada da, kafa Hukumar Samar Da Ayyukan Yi ga Matasa ta Jihar Jigawa wato (YEEA), domin magance kalubalen rashin aikin yi a jihar.

Wannan hukumar ta bude wani shafin Intanet da ya yadu a jihar domin matasa su rika dora bayanansu wajen nemo matasa marasa aikin yi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

A cikin dan kankanin lokacin da wannan hukuma ta fara aiki, ta horar da matasa sama da 100,000 horo kan shirye-shiryen koyon sana’o’i daban-daban a fannonin noma, ICT, kananan sana’o’i da dai sauran su, gwamnatin jihar ta bayar da tallafi da jarin sama da Naira biliyan 1.7 ga wadannan matasa domin fara sana’o’i. Har ila yau, ya saukaka wa wadannan matasa rayuwa sa suka cancanta a cikin jihohi da tarayya.

Jihar jigawa jiha ce mai girma ta kuma yi fice a fannin noma a kokarin gwamnati na inganta rayuwar al’umma ta hanyar sabbin manufofin noma da ya zama abin a yaba.

Domin tabbatar da samar da wadataccen kayan aikin noma akai-akai, gwamnatin jihar ta zuba Naira biliyan 5 ga kamfanin samar da aikin gona na Jihar Jigawa (JASCO).

Haka zalika, Gwamnatin Namadi ta samar da sabbin tsare-tsare a fannin noma ta hanyar inganta tsarin samar da shinkafa, alkama, sesame da hibiscus domin bunkasa yankunan jihar.

A tsawon lokacin da ake bitar, jihar ta sayi tan 9,200 na taki, tarakta 60, tare da motocin girbi 10 gami da samar da fili mai fadin hekta 40,000 don shirin noman alkama wanda ya zama hadin gwiwa ne da gwamnatin tarayya.

Gwamnatin jihar ta kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna MOU da Bankin Duniya, Bankin Raya Afirka da Bankin Raya Musulunci a fannin noma da dai sauransu.

Haka kuma ayyukan da gwamnatin Namadi ta yi a fannin ilimi ba boyayye ba ne.

Shi ne Gwamna daya tilo a Nijeriya da ya zarce shawarar da UNESCO ta bayar na samar da kaso 25 a kasafin kudi ta fannin ilimi, wanda wannan shi ne karon farko da aka samu a tarinhin Jihar Jigawa da watakila a Arewacin Nijeriya.

Sannan Gwamna Namadi ya ware kashi 32 na kasafin kudi wa fannin ilimi, wanda ba kasafai ake samu ba a Nijeriya. Ya kara wa dalibai tallafin karatu da kashi 100 yayin da ya kara kudin ciyar da dalibai da kashi 40 cikin 100.

Har ila yau, gwamnatinsa ta dauki dalibai 150 da suka kammala karatun digiri na farko a jihar a matsayin malamai a manyan makarantun jihar yayin da aka bai wa malamai 3,570 aikin yi a makarantun firamare da sakandare a fadin jihar ta hanyar shirin J-Teach. haka kuma gwamnati ta gina manyan makarantun sakandare a jihar .

Domin magance matsalar yara da ba sa zuwa makaranta, gwamnatin ta bullo da sabbin makarantu na Mega Tsangaya tare da cibiyoyin ilimi da fasaha na yammacin Turai don magance wannan matsalar.

Jihar ta kuma hada gwiwa da hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta Nijeriya NITDA, domin horo gami da zurfafa ilimin malaman Jigawa da basu kwarewa ta fasahar sadarwa ICT saboda bunkasa fasaharsu ta koyarwa.

Bugu da kari, a fannin lafiya an samu sauye-sauye da dama a wannan bangare da ya shafi ma’aikatan lafiya a jihar inda aka fitar da Naira biliyan 17.2 domin kammala ayyukan asibitoci daban-daban a fadin jihar.

Gwamnatin ta kuma fitar da asusun kula da lafiya na Naira biliyan 1.2 domin kafa tsarin kiwon lafiya na Inshora ga gidaje sama da 140,000 tare da mutane 500 da suka cancanta a dukkan gundumomi 287 da ke fadin jihar.

Gwamnatin jihar ta shirya gina Cibiyar Kula da Lafiya a Matakin Farko a kowace Unguwa da kuma Babban Asibiti daya a kowace mazaba.

Gwamna Namadi ya kuma jajirce wajen tunkarar kalubalen da talakawa da marasa galihu ke fuskanta a cikin al’umma. Ya sanya an gudanar da kidayar gidajen marayu, nakasassu, tsofaffi da sauran su domin taimaka musu, sannan ya kara alawus din Tsaron Jama’a daga Naira 7000 zuwa 10,000.

Wani bangare na rangadin da Gwamnan ya fara a duk fadin yankin mazabu shi ne, jin ta bakin talakawa kai tsaye domin samar da mafita mai dorewa ga marasa galihu a cikin al’ummarmu.

Haka kuma gwamna ya sake samar da wasu tsare-tsare a fannin lafiya domin saukaka wa majinyata masu fama da cutuka masu tsanani kamar su ciwon koda, ciwon daji da kuma hanta a jihar ta hanyar biyan kudaden majinyatan da suka jima da larurar domin ganin sun warke daga cutar.

A kasa da shekaru biyu, Gwamna Namadi ya nuna kwarewa, iya aiki da kuma jajircewa wajen inganta rayuwar al’ummar jihar kuma sakamakon hakan ne yake ta samun lambobin yabo na karramawa a fadin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna NamadiJigawaMatakai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno

Next Post

Xi: Daukar Matsayar Kashin Kai Da Danniya Ba Za Su Taba Samun Goyon Bayan Al’umma Ba

Related

Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

4 weeks ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

4 weeks ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

4 weeks ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

4 weeks ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Fursunoni 48,932 Ke Jiran Shari’a A Gidajen Yarin Nijeriya – Mukaddaashin Kwantirola
Rahotonni

Fursunoni 48,932 Ke Jiran Shari’a A Gidajen Yarin Nijeriya – Mukaddaashin Kwantirola

3 months ago
Next Post
Xi: Daukar Matsayar Kashin Kai Da Danniya Ba Za Su Taba Samun Goyon Bayan Al’umma Ba

Xi: Daukar Matsayar Kashin Kai Da Danniya Ba Za Su Taba Samun Goyon Bayan Al’umma Ba

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.