Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayar da gudunmuwar Naira miliyan 300 ga wadanda bala’in ambaliyar ruwa ta Mokwa ta shafa.
Gwamnan ya sanar da bayar da tallafin ne a lokacin da ya jagoranci wata tawaga daga Borno a ziyarar jaje da suka kai gidan gwamnati, ranar Talata a Minna, jihar Neja.
Zulum ya bayyana cewa, an bayar da tallafin ne domin kara kaimi ga kokarin gwamnatin Neja na magance kalubalen da bala’in ya haifar.
Gwamnan ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Neja kan mummunar barnar da ambaliyar ruwan ta yi, na salwantar da rayuka da barnata dukiya da dama.
Gwamna Umar Bago na jihar Neja, ya yabawa takwaransa na Borno bisa wannan ziyarar da kuma bayar da gudunmawar, inda ya ce lokaci ya yi da za a nuna soyayya ga juna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp