ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
Siyasa

‘Yan siyasa da magoya bayansu sun ci gaba da watsi da gargadin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) ta yi na gudanar da yakin neman zaben 2027.

Duk da umarnin da INEC ta bayar, siyasa tana kara yin zafi a tsakanin masu neman takara da magoya bayansu, yayin da suke kara daukar matakai na tallata burikansu da yin sharyi kan zaben 2027. Yanayin siyasa na kara zafafa a daidai lokacin da ya rage saura shekara biyu a yi zabe a Nijeriya.

Manyan ‘yan siyasa sun fara yin bayani da ke bayyana aniyarsu ta tsayawa takara, yayin da suke kuma neman goyon baya ga masu ruwa da tsaki daban-daban.

ADVERTISEMENT

Musamman a matakin kasa, jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Shugaba Bola Tinubu a matsayin dan takarar shugaban kasa guda daya tilo a zaben 2027, bayan samun goyon baya daga manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, wato kwamitin zartarwa na kasada kuma na yankuna.

A taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar da aka gudanar a ranar 26 ga Fabrairu, 2025, APC ta amince da tazarcen Shugaba Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

A wannan rana, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya gabatar da kudrin goyon bayan tazarcen Tinubu. Nan take tsohon gwamnan Jihar Edo da kuma dan majalisar dattawa, Sanata Adams Oshiomhole ya amince da kudirin.

Bayan wata uku, kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC ya bayyana shugaban kasa Tinubu a matsayin dan takarar daya tilo na shugaban kasa a zaben 2027.

Haka nan a taron kungiyar gwamnonin APC da ‘yan majalisaun tarayya na jam’iyyar sun amince da Shugaba Tinubu a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a zaben 2027.

Kazalika, dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya tabbatar da niyyarsa na sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027, tare da alkawarin yin wa’adi guda na shekaru hudu idan aka zabe shi.

Obi ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita, inda ya amsa tambayoyin daga masu goyon baya a gida Nijeriya da kuma kasashen waje. Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya yi alkawarin sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Hak kuma, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, ya bayyana niyyarsa ta takarar shugabancin kasa a 2027, yana bayyana kwarin gwiwar cewa zai iya kayar da Shugaba Tinubu a zaben 2027, idan ya samu tikitin tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC.

Amaechi, ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da aka yi da shi a Shafin Tuwita, ya roki jam’iyyar ADC da su ba shi tikitin takarar shugaban kasa, yana mai jaddada cewa shi ya san lagon karya Shugaba Tinubu da jam’iyyarsa ta APC mai mulki.

Wani bidiyon da ake yadawa kwanan nan game da yiwuwar neman takarar shugaban kasa a 2027 na tsohon dan takarar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar. Masu sharhi da yawa sun fassara wannan bidiyon a matsayin wata alama ta nufin sake fitowa takara. Duk da haka, mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya musanta ikirarin, yana mai cewa bidiyon an dauke shi ne a 2022, kafin zaben fid da gwani na PDP.

A halin yanzu, a yankin arewa ta tsakiyar, kungiyar shugabannin matasa ta goyi bayan shahararren dan kasuwa, Dakta Gbenga Olawepo-Hashim, a matsayin dan takararsu na shugaban kasa a 2027.

Sun bayyana boyon bayan nasu ne a lokacin taron manema labarai a Abuja, wanda kungiyar matasa na arewa tsakiya (YANCP) ta shirya, ta kasance wata kungiya da ke nuna goyon bayan shugabanci ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya a 2027.

Sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, wanda ya ce jam’iyyun siyasa ba za su fara gudanar da yakin neman zabe ba a bainar jama’a har sai kwanaki 150 kafin ranar zabe kuma ba su wuce sa’o’i 24 kafin wannan ranar ba.

Babban sakataren yada labarai na INEC, Rotimi Oyekanmi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa rashin dacewa da kuma rashin bin doka ne ga kowace jam’iyya ta siyasa ta fara gudanar da yakin neman zaben 2027 a wannan lokacin, wanda hakan ya saba wa dokar zabe ta 2022.

“Babu wani tanadi na musamman a cikin dokar zabe ta 2022 da ke haramta goyon bayan ‘yan takara a wurin mutane da kungiyoyi wajen zabe.

“A karkashin sashe na 94(1) na dokar zabe ta 2022, jam’iyyun siyasa ba za su fara yakin neman zabe ba har sai ya rage saura kwana 150 kafin ranar zabe kuma za a dakata a kafin awanni 24 kafin wannan rana.

“Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta saki jadawalin ayyukan zaben 2027 ba, wanda zai bayyana lokacin kamfen ga jam’iyyun siyasa a fili. Saboda haka, zai zama saba wa doka ga kowace jam’iyya ta fara yakin neman zaben 2027 a wannan lokaci,” in ji shi.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
Labarai

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Next Post
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.