ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, a ranar Litinin ya kaddamar da shimfida hanya mai nisan kilomita 19 da ta tashi daga garin Liman Katagum ta nufi garin Luda zuwa Lekka da ke cikin karamar hukumar Bauchi.

Aikin wanda zai lakume naira Biliyan N2,400,000,000 zai gudana ne bisa hadin guiwa da babban bankin duniya ta karkashin shirin bunkasa hanyoyin karkara (RAAMP).

  • Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Da ya ke kaddamar da aikin, gwamna Bala Muhammad, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da inganta rayuwar al’ummar karkara ta hanyoyi daban-daban musamman na samar musu da hanyoyin tituna da za su hadesu da sauran al’ummomi domin bunkasa harkokin kasuwancinsu da hada-hadar yau da gobe.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, nan ba da jimawa ba, gwamnatinsa za ta cigaba da shimfida ayyukan titina da dama domin kara saukaka wa matafiya da kuma bunkasa harkokin tattalin arziki a sassan jihar.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

Bala ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin babban bankin duniya, ya kuma gargadi dan kwangilar da aka ba shi aikin da ya tabbatar da ya yi aiki mai nagarta da inganci, yana mai cewa da kansa zai ke bibiyar aiki domin tabbatar da an yi mai inganci.

Gwamnan, ya ce, da zarar aka kammala aikin hanyar Liman Katagum-Luda-Lekka, zai kawo karshen matsalolin da manoma suke fuskanta na fitar da amfanin gonarsu na tsawon shekaru, kuma a cewarsa, hakan zai taimaka wajen bunkasa kiwon lafiya, harkokin ilimi, jin dadi da walwalar al’umman yankin.

Tun da farko a jawabinsa, kwamishinan ayyukan musamman da raya yankunan karkara na jihar Bauchi, Hon. Farouk Mustapha, ya ce, bayan kammala aikin hanyar, hanyar za ta hade al’ummomin Liman Katagum, Luda da Lekka hadi da sauran kauyukan da ke yankunan kuma za a samu bunkasar tattalin arziki.

Faruk ya ce, ana sa ran karkashin shirin RAAMP jihar Bauchi za ta ci gajiyar hanyoyi da nisansu ya kai na kilimiya sama da dubu a sassa daban-daban.

A nata bangaren, shugaban riko na karamar hukumar Bauchi, Hajiya Zainab Baban Tanko, ta nuna matukar godiyarta ne ga gwamnan bisa tsayuwar dakar da yake yi wajen ganin ya kyautata rayuwar al’ummar jiha da na karkara.

Ta nuna cewa, tsawon lokaci al’ummar wannan yankin suna bukatar wannan hanyar don haka ta nuna farin cikin da al’umman ke ciki dangane da fara aikin hanyar.

Bauchi

Ta bukaci al’umman yankin da su bayar da hadin kai domin cimma nasarar aikin a daidai lokacin da aka tsara.

Shi kuma a nasa bigiren, Ko’odinetan shirin RAAMP, Injiniya Aminu Muhammad Bodinga, ya ce, jihar Bauchi na daga cikin jihohi 19 da za su amfana da shirin bayan cika ka’idojin da shirin ke bukata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
Next Post
Mataimakin shugaban kasa

Tinubu Ya Amince Da Nadin Hadimai 18 Ga Mataimakin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.