ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, a ranar Litinin ya kaddamar da shimfida hanya mai nisan kilomita 19 da ta tashi daga garin Liman Katagum ta nufi garin Luda zuwa Lekka da ke cikin karamar hukumar Bauchi.

Aikin wanda zai lakume naira Biliyan N2,400,000,000 zai gudana ne bisa hadin guiwa da babban bankin duniya ta karkashin shirin bunkasa hanyoyin karkara (RAAMP).

  • Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Da ya ke kaddamar da aikin, gwamna Bala Muhammad, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da inganta rayuwar al’ummar karkara ta hanyoyi daban-daban musamman na samar musu da hanyoyin tituna da za su hadesu da sauran al’ummomi domin bunkasa harkokin kasuwancinsu da hada-hadar yau da gobe.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, nan ba da jimawa ba, gwamnatinsa za ta cigaba da shimfida ayyukan titina da dama domin kara saukaka wa matafiya da kuma bunkasa harkokin tattalin arziki a sassan jihar.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Bala ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin babban bankin duniya, ya kuma gargadi dan kwangilar da aka ba shi aikin da ya tabbatar da ya yi aiki mai nagarta da inganci, yana mai cewa da kansa zai ke bibiyar aiki domin tabbatar da an yi mai inganci.

Gwamnan, ya ce, da zarar aka kammala aikin hanyar Liman Katagum-Luda-Lekka, zai kawo karshen matsalolin da manoma suke fuskanta na fitar da amfanin gonarsu na tsawon shekaru, kuma a cewarsa, hakan zai taimaka wajen bunkasa kiwon lafiya, harkokin ilimi, jin dadi da walwalar al’umman yankin.

Tun da farko a jawabinsa, kwamishinan ayyukan musamman da raya yankunan karkara na jihar Bauchi, Hon. Farouk Mustapha, ya ce, bayan kammala aikin hanyar, hanyar za ta hade al’ummomin Liman Katagum, Luda da Lekka hadi da sauran kauyukan da ke yankunan kuma za a samu bunkasar tattalin arziki.

Faruk ya ce, ana sa ran karkashin shirin RAAMP jihar Bauchi za ta ci gajiyar hanyoyi da nisansu ya kai na kilimiya sama da dubu a sassa daban-daban.

A nata bangaren, shugaban riko na karamar hukumar Bauchi, Hajiya Zainab Baban Tanko, ta nuna matukar godiyarta ne ga gwamnan bisa tsayuwar dakar da yake yi wajen ganin ya kyautata rayuwar al’ummar jiha da na karkara.

Ta nuna cewa, tsawon lokaci al’ummar wannan yankin suna bukatar wannan hanyar don haka ta nuna farin cikin da al’umman ke ciki dangane da fara aikin hanyar.

Bauchi

Ta bukaci al’umman yankin da su bayar da hadin kai domin cimma nasarar aikin a daidai lokacin da aka tsara.

Shi kuma a nasa bigiren, Ko’odinetan shirin RAAMP, Injiniya Aminu Muhammad Bodinga, ya ce, jihar Bauchi na daga cikin jihohi 19 da za su amfana da shirin bayan cika ka’idojin da shirin ke bukata.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Mataimakin shugaban kasa

Tinubu Ya Amince Da Nadin Hadimai 18 Ga Mataimakin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.