ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, a ranar Litinin ya kaddamar da shimfida hanya mai nisan kilomita 19 da ta tashi daga garin Liman Katagum ta nufi garin Luda zuwa Lekka da ke cikin karamar hukumar Bauchi.

Aikin wanda zai lakume naira Biliyan N2,400,000,000 zai gudana ne bisa hadin guiwa da babban bankin duniya ta karkashin shirin bunkasa hanyoyin karkara (RAAMP).

  • Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Da ya ke kaddamar da aikin, gwamna Bala Muhammad, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da inganta rayuwar al’ummar karkara ta hanyoyi daban-daban musamman na samar musu da hanyoyin tituna da za su hadesu da sauran al’ummomi domin bunkasa harkokin kasuwancinsu da hada-hadar yau da gobe.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, nan ba da jimawa ba, gwamnatinsa za ta cigaba da shimfida ayyukan titina da dama domin kara saukaka wa matafiya da kuma bunkasa harkokin tattalin arziki a sassan jihar.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Bala ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin babban bankin duniya, ya kuma gargadi dan kwangilar da aka ba shi aikin da ya tabbatar da ya yi aiki mai nagarta da inganci, yana mai cewa da kansa zai ke bibiyar aiki domin tabbatar da an yi mai inganci.

Gwamnan, ya ce, da zarar aka kammala aikin hanyar Liman Katagum-Luda-Lekka, zai kawo karshen matsalolin da manoma suke fuskanta na fitar da amfanin gonarsu na tsawon shekaru, kuma a cewarsa, hakan zai taimaka wajen bunkasa kiwon lafiya, harkokin ilimi, jin dadi da walwalar al’umman yankin.

Tun da farko a jawabinsa, kwamishinan ayyukan musamman da raya yankunan karkara na jihar Bauchi, Hon. Farouk Mustapha, ya ce, bayan kammala aikin hanyar, hanyar za ta hade al’ummomin Liman Katagum, Luda da Lekka hadi da sauran kauyukan da ke yankunan kuma za a samu bunkasar tattalin arziki.

Faruk ya ce, ana sa ran karkashin shirin RAAMP jihar Bauchi za ta ci gajiyar hanyoyi da nisansu ya kai na kilimiya sama da dubu a sassa daban-daban.

A nata bangaren, shugaban riko na karamar hukumar Bauchi, Hajiya Zainab Baban Tanko, ta nuna matukar godiyarta ne ga gwamnan bisa tsayuwar dakar da yake yi wajen ganin ya kyautata rayuwar al’ummar jiha da na karkara.

Ta nuna cewa, tsawon lokaci al’ummar wannan yankin suna bukatar wannan hanyar don haka ta nuna farin cikin da al’umman ke ciki dangane da fara aikin hanyar.

Bauchi

Ta bukaci al’umman yankin da su bayar da hadin kai domin cimma nasarar aikin a daidai lokacin da aka tsara.

Shi kuma a nasa bigiren, Ko’odinetan shirin RAAMP, Injiniya Aminu Muhammad Bodinga, ya ce, jihar Bauchi na daga cikin jihohi 19 da za su amfana da shirin bayan cika ka’idojin da shirin ke bukata.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Mataimakin shugaban kasa

Tinubu Ya Amince Da Nadin Hadimai 18 Ga Mataimakin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.