ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, a ranar Litinin ya kaddamar da shimfida hanya mai nisan kilomita 19 da ta tashi daga garin Liman Katagum ta nufi garin Luda zuwa Lekka da ke cikin karamar hukumar Bauchi.

Aikin wanda zai lakume naira Biliyan N2,400,000,000 zai gudana ne bisa hadin guiwa da babban bankin duniya ta karkashin shirin bunkasa hanyoyin karkara (RAAMP).

  • Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Da ya ke kaddamar da aikin, gwamna Bala Muhammad, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da inganta rayuwar al’ummar karkara ta hanyoyi daban-daban musamman na samar musu da hanyoyin tituna da za su hadesu da sauran al’ummomi domin bunkasa harkokin kasuwancinsu da hada-hadar yau da gobe.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, nan ba da jimawa ba, gwamnatinsa za ta cigaba da shimfida ayyukan titina da dama domin kara saukaka wa matafiya da kuma bunkasa harkokin tattalin arziki a sassan jihar.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Bala ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin babban bankin duniya, ya kuma gargadi dan kwangilar da aka ba shi aikin da ya tabbatar da ya yi aiki mai nagarta da inganci, yana mai cewa da kansa zai ke bibiyar aiki domin tabbatar da an yi mai inganci.

Gwamnan, ya ce, da zarar aka kammala aikin hanyar Liman Katagum-Luda-Lekka, zai kawo karshen matsalolin da manoma suke fuskanta na fitar da amfanin gonarsu na tsawon shekaru, kuma a cewarsa, hakan zai taimaka wajen bunkasa kiwon lafiya, harkokin ilimi, jin dadi da walwalar al’umman yankin.

Tun da farko a jawabinsa, kwamishinan ayyukan musamman da raya yankunan karkara na jihar Bauchi, Hon. Farouk Mustapha, ya ce, bayan kammala aikin hanyar, hanyar za ta hade al’ummomin Liman Katagum, Luda da Lekka hadi da sauran kauyukan da ke yankunan kuma za a samu bunkasar tattalin arziki.

Faruk ya ce, ana sa ran karkashin shirin RAAMP jihar Bauchi za ta ci gajiyar hanyoyi da nisansu ya kai na kilimiya sama da dubu a sassa daban-daban.

A nata bangaren, shugaban riko na karamar hukumar Bauchi, Hajiya Zainab Baban Tanko, ta nuna matukar godiyarta ne ga gwamnan bisa tsayuwar dakar da yake yi wajen ganin ya kyautata rayuwar al’ummar jiha da na karkara.

Ta nuna cewa, tsawon lokaci al’ummar wannan yankin suna bukatar wannan hanyar don haka ta nuna farin cikin da al’umman ke ciki dangane da fara aikin hanyar.

Bauchi

Ta bukaci al’umman yankin da su bayar da hadin kai domin cimma nasarar aikin a daidai lokacin da aka tsara.

Shi kuma a nasa bigiren, Ko’odinetan shirin RAAMP, Injiniya Aminu Muhammad Bodinga, ya ce, jihar Bauchi na daga cikin jihohi 19 da za su amfana da shirin bayan cika ka’idojin da shirin ke bukata.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Mataimakin shugaban kasa

Tinubu Ya Amince Da Nadin Hadimai 18 Ga Mataimakin Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.