• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya amince da nadin mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya OON, a matsayin wanda zai jagoranci aikin hajjin bana wato ‘Amirul Hajji’ na 2023.

Sakataren gwamnatin jihar Bauchi, Ibrahim Muhammad Kashim, shi ne wanda ya sanar da nadin na gwamnan, ya shaida cewar nadin kuma zai fara aiki ne nan take.

  • Da Dumi-Dumi: Sanata Abdul Ningi Ya Lashe Zaben Sanatan Bauchi Ta Tsakiya
  • Kauran Bauchi Zai Gyara Kasuwar Katako Da Gobara Ta Kone Da Tallafin Miliyan 10

A cewarsa, nadin Alhaji Danyaya da sauran muhimman mambobi su 24 ‘yan asalin jihar da za su kasance a tawagar, an yi ne bisa kyakkyawar tarihinsu da aikinsu tukuru, himma, kwazo, kishin kasa, rikon amana, jajircewa da kuma tsohon Allah dinsu.

Bala ya bukaci mambobin tawagar da su yi aiki tukuru wajen sauke nauyin da ke kansu tare da tabbatar da sun gamsar da irin yardan da gwamnati da al’ummar jihar suka musu.

Kamar yadda Malam Mukhtar Gidado, kakakin gwamnan jihar, ya fitar ta cikin wata sanarwa a daren jiya Juma’a, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za su yi aiki kafada-da-kafada da hukumar jin dadin alhazai ta jihar, da sauran hukumomin da lamarin ya shafa na jiha, kasa da ma kasashen waje domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin bana cikin kwanciyar hankali da nasara.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Kazalika, mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi, Rt. Hon. Danlami Ahmed Kawule shi ne zai kasance mataimakin Amirul Hajjin a bana.

Sauran mambobi sun hada da: Mai shari’a Rabi Talatu Umar, babban jojin jihar Bauchi; Hon. Khadi Umar Liman Grand Khadi na jihar Bauchi; Imam Bala Ahmed Baban Inna, babban limamin Bauchi; Hon. Tijjani Mohammed Aliyu, shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Bauchi; Hon. Bakoji Aliyu Bobbo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar; Hon. Bala Abdullahi Dan na BAHA.

Saura su ne: Hon. Umar Babayo Kesa, kwamishinan ma’aikatar harkokin addinai; Hon. Abdulrazak Nuhu Zaki, kwamishinan ma’aikatar kula da harkokin kananan hukumomi da masarautun gargajiya.

Sauran mambobin sun kunshi: Alhaji Ibrahim Y.M. Baba, Sarkin Duguri; Alhaji Aliyu Yakubu Lame, Sarkin Yakin Bauchi; Alhaji Bala Sulaiman Adamu, Dan Galadiman Bauchi; Alhaji Iliyasu Aliyu, Hakimin kasar Akuyam; Alhaji Umar Ibrahim, Sarkin Shira; Alhaji Yayanuwa Zainabari, sakataren watsa labarai na PDP a jihar Bauchi; Sheikh Salisu Sulaiman Ningi; Barista Garba Hassan; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Malam Mustapha Baba Ilelah, shugaban hukumar shari’a ta jihar Bauchi; Alaramma Zakari Ya’u Dan-Yusuf Dauduwo; Ahmed Inuwa Na’ibi, mataimakin babban limamnin Bauchi da Alhaji Bala Hadith jigo a jam’iyyar PDP.

A fadin sanarwar, Yahaya Abubakar Umar shi ne zai yi aiki a matsayin sakataren tawagar Alhazan yayin da kuma Aliyu Adamu Abdulkadir zai yi aiki a matsayin mataimakinsa sakataren.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amirul HajjBauchiNingiSarkin Ningi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hana Likitoci Fita Wajen Nijeriya Danyen Aiki Ne – Shugaban NANNM

Next Post

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

20 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

1 hour ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

2 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

4 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

6 hours ago
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.