ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya amince da nadin mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya OON, a matsayin wanda zai jagoranci aikin hajjin bana wato ‘Amirul Hajji’ na 2023.

Sakataren gwamnatin jihar Bauchi, Ibrahim Muhammad Kashim, shi ne wanda ya sanar da nadin na gwamnan, ya shaida cewar nadin kuma zai fara aiki ne nan take.

  • Da Dumi-Dumi: Sanata Abdul Ningi Ya Lashe Zaben Sanatan Bauchi Ta Tsakiya
  • Kauran Bauchi Zai Gyara Kasuwar Katako Da Gobara Ta Kone Da Tallafin Miliyan 10

A cewarsa, nadin Alhaji Danyaya da sauran muhimman mambobi su 24 ‘yan asalin jihar da za su kasance a tawagar, an yi ne bisa kyakkyawar tarihinsu da aikinsu tukuru, himma, kwazo, kishin kasa, rikon amana, jajircewa da kuma tsohon Allah dinsu.

ADVERTISEMENT

Bala ya bukaci mambobin tawagar da su yi aiki tukuru wajen sauke nauyin da ke kansu tare da tabbatar da sun gamsar da irin yardan da gwamnati da al’ummar jihar suka musu.

Kamar yadda Malam Mukhtar Gidado, kakakin gwamnan jihar, ya fitar ta cikin wata sanarwa a daren jiya Juma’a, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za su yi aiki kafada-da-kafada da hukumar jin dadin alhazai ta jihar, da sauran hukumomin da lamarin ya shafa na jiha, kasa da ma kasashen waje domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin bana cikin kwanciyar hankali da nasara.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Kazalika, mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi, Rt. Hon. Danlami Ahmed Kawule shi ne zai kasance mataimakin Amirul Hajjin a bana.

Sauran mambobi sun hada da: Mai shari’a Rabi Talatu Umar, babban jojin jihar Bauchi; Hon. Khadi Umar Liman Grand Khadi na jihar Bauchi; Imam Bala Ahmed Baban Inna, babban limamin Bauchi; Hon. Tijjani Mohammed Aliyu, shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Bauchi; Hon. Bakoji Aliyu Bobbo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar; Hon. Bala Abdullahi Dan na BAHA.

Saura su ne: Hon. Umar Babayo Kesa, kwamishinan ma’aikatar harkokin addinai; Hon. Abdulrazak Nuhu Zaki, kwamishinan ma’aikatar kula da harkokin kananan hukumomi da masarautun gargajiya.

Sauran mambobin sun kunshi: Alhaji Ibrahim Y.M. Baba, Sarkin Duguri; Alhaji Aliyu Yakubu Lame, Sarkin Yakin Bauchi; Alhaji Bala Sulaiman Adamu, Dan Galadiman Bauchi; Alhaji Iliyasu Aliyu, Hakimin kasar Akuyam; Alhaji Umar Ibrahim, Sarkin Shira; Alhaji Yayanuwa Zainabari, sakataren watsa labarai na PDP a jihar Bauchi; Sheikh Salisu Sulaiman Ningi; Barista Garba Hassan; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Malam Mustapha Baba Ilelah, shugaban hukumar shari’a ta jihar Bauchi; Alaramma Zakari Ya’u Dan-Yusuf Dauduwo; Ahmed Inuwa Na’ibi, mataimakin babban limamnin Bauchi da Alhaji Bala Hadith jigo a jam’iyyar PDP.

A fadin sanarwar, Yahaya Abubakar Umar shi ne zai yi aiki a matsayin sakataren tawagar Alhazan yayin da kuma Aliyu Adamu Abdulkadir zai yi aiki a matsayin mataimakinsa sakataren.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.