ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya amince da nadin mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya OON, a matsayin wanda zai jagoranci aikin hajjin bana wato ‘Amirul Hajji’ na 2023.

Sakataren gwamnatin jihar Bauchi, Ibrahim Muhammad Kashim, shi ne wanda ya sanar da nadin na gwamnan, ya shaida cewar nadin kuma zai fara aiki ne nan take.

  • Da Dumi-Dumi: Sanata Abdul Ningi Ya Lashe Zaben Sanatan Bauchi Ta Tsakiya
  • Kauran Bauchi Zai Gyara Kasuwar Katako Da Gobara Ta Kone Da Tallafin Miliyan 10

A cewarsa, nadin Alhaji Danyaya da sauran muhimman mambobi su 24 ‘yan asalin jihar da za su kasance a tawagar, an yi ne bisa kyakkyawar tarihinsu da aikinsu tukuru, himma, kwazo, kishin kasa, rikon amana, jajircewa da kuma tsohon Allah dinsu.

ADVERTISEMENT

Bala ya bukaci mambobin tawagar da su yi aiki tukuru wajen sauke nauyin da ke kansu tare da tabbatar da sun gamsar da irin yardan da gwamnati da al’ummar jihar suka musu.

Kamar yadda Malam Mukhtar Gidado, kakakin gwamnan jihar, ya fitar ta cikin wata sanarwa a daren jiya Juma’a, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za su yi aiki kafada-da-kafada da hukumar jin dadin alhazai ta jihar, da sauran hukumomin da lamarin ya shafa na jiha, kasa da ma kasashen waje domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin bana cikin kwanciyar hankali da nasara.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Kazalika, mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi, Rt. Hon. Danlami Ahmed Kawule shi ne zai kasance mataimakin Amirul Hajjin a bana.

Sauran mambobi sun hada da: Mai shari’a Rabi Talatu Umar, babban jojin jihar Bauchi; Hon. Khadi Umar Liman Grand Khadi na jihar Bauchi; Imam Bala Ahmed Baban Inna, babban limamin Bauchi; Hon. Tijjani Mohammed Aliyu, shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Bauchi; Hon. Bakoji Aliyu Bobbo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar; Hon. Bala Abdullahi Dan na BAHA.

Saura su ne: Hon. Umar Babayo Kesa, kwamishinan ma’aikatar harkokin addinai; Hon. Abdulrazak Nuhu Zaki, kwamishinan ma’aikatar kula da harkokin kananan hukumomi da masarautun gargajiya.

Sauran mambobin sun kunshi: Alhaji Ibrahim Y.M. Baba, Sarkin Duguri; Alhaji Aliyu Yakubu Lame, Sarkin Yakin Bauchi; Alhaji Bala Sulaiman Adamu, Dan Galadiman Bauchi; Alhaji Iliyasu Aliyu, Hakimin kasar Akuyam; Alhaji Umar Ibrahim, Sarkin Shira; Alhaji Yayanuwa Zainabari, sakataren watsa labarai na PDP a jihar Bauchi; Sheikh Salisu Sulaiman Ningi; Barista Garba Hassan; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Malam Mustapha Baba Ilelah, shugaban hukumar shari’a ta jihar Bauchi; Alaramma Zakari Ya’u Dan-Yusuf Dauduwo; Ahmed Inuwa Na’ibi, mataimakin babban limamnin Bauchi da Alhaji Bala Hadith jigo a jam’iyyar PDP.

A fadin sanarwar, Yahaya Abubakar Umar shi ne zai yi aiki a matsayin sakataren tawagar Alhazan yayin da kuma Aliyu Adamu Abdulkadir zai yi aiki a matsayin mataimakinsa sakataren.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.