ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya amince da nadin mai martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammad Danyaya OON, a matsayin wanda zai jagoranci aikin hajjin bana wato ‘Amirul Hajji’ na 2023.

Sakataren gwamnatin jihar Bauchi, Ibrahim Muhammad Kashim, shi ne wanda ya sanar da nadin na gwamnan, ya shaida cewar nadin kuma zai fara aiki ne nan take.

  • Da Dumi-Dumi: Sanata Abdul Ningi Ya Lashe Zaben Sanatan Bauchi Ta Tsakiya
  • Kauran Bauchi Zai Gyara Kasuwar Katako Da Gobara Ta Kone Da Tallafin Miliyan 10

A cewarsa, nadin Alhaji Danyaya da sauran muhimman mambobi su 24 ‘yan asalin jihar da za su kasance a tawagar, an yi ne bisa kyakkyawar tarihinsu da aikinsu tukuru, himma, kwazo, kishin kasa, rikon amana, jajircewa da kuma tsohon Allah dinsu.

ADVERTISEMENT

Bala ya bukaci mambobin tawagar da su yi aiki tukuru wajen sauke nauyin da ke kansu tare da tabbatar da sun gamsar da irin yardan da gwamnati da al’ummar jihar suka musu.

Kamar yadda Malam Mukhtar Gidado, kakakin gwamnan jihar, ya fitar ta cikin wata sanarwa a daren jiya Juma’a, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za su yi aiki kafada-da-kafada da hukumar jin dadin alhazai ta jihar, da sauran hukumomin da lamarin ya shafa na jiha, kasa da ma kasashen waje domin tabbatar da an gudanar da aikin hajjin bana cikin kwanciyar hankali da nasara.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Kazalika, mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi, Rt. Hon. Danlami Ahmed Kawule shi ne zai kasance mataimakin Amirul Hajjin a bana.

Sauran mambobi sun hada da: Mai shari’a Rabi Talatu Umar, babban jojin jihar Bauchi; Hon. Khadi Umar Liman Grand Khadi na jihar Bauchi; Imam Bala Ahmed Baban Inna, babban limamin Bauchi; Hon. Tijjani Mohammed Aliyu, shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Bauchi; Hon. Bakoji Aliyu Bobbo, shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar; Hon. Bala Abdullahi Dan na BAHA.

Saura su ne: Hon. Umar Babayo Kesa, kwamishinan ma’aikatar harkokin addinai; Hon. Abdulrazak Nuhu Zaki, kwamishinan ma’aikatar kula da harkokin kananan hukumomi da masarautun gargajiya.

Sauran mambobin sun kunshi: Alhaji Ibrahim Y.M. Baba, Sarkin Duguri; Alhaji Aliyu Yakubu Lame, Sarkin Yakin Bauchi; Alhaji Bala Sulaiman Adamu, Dan Galadiman Bauchi; Alhaji Iliyasu Aliyu, Hakimin kasar Akuyam; Alhaji Umar Ibrahim, Sarkin Shira; Alhaji Yayanuwa Zainabari, sakataren watsa labarai na PDP a jihar Bauchi; Sheikh Salisu Sulaiman Ningi; Barista Garba Hassan; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Malam Mustapha Baba Ilelah, shugaban hukumar shari’a ta jihar Bauchi; Alaramma Zakari Ya’u Dan-Yusuf Dauduwo; Ahmed Inuwa Na’ibi, mataimakin babban limamnin Bauchi da Alhaji Bala Hadith jigo a jam’iyyar PDP.

A fadin sanarwar, Yahaya Abubakar Umar shi ne zai yi aiki a matsayin sakataren tawagar Alhazan yayin da kuma Aliyu Adamu Abdulkadir zai yi aiki a matsayin mataimakinsa sakataren.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.