ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Faston

Shugaba cocin nan na Kenya da ake zargi da laifin tilasta wa mabiyansa azumin mutuwa don haduwa da Yesu Almasihu ya sake bayyana a gaban kotu ranar Larabar nan, bayan gurfana da ya yi a ranar Talata.

Hukumomi na gudanar da bincike kan yiwuwar cewa an yi amfani da sassan jikin mutanen da suka mutun.

  • Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo
  • Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Binciken ‘yan sanda ya nuna yadda aka gano karin wasu gawawwakin da aka cire sassan jikinsu.

ADVERTISEMENT

 Wannan ya sa ake ganin da alama an yi amfani da sassan jikin gawawwakin mabiyan na Cocin Good News International, da aka gano a dajin Shakahola na kasar ta Kenya.

Kusan a kullum aka ci gaba da binciken da ake yi tun da aka fara gano wannan al’amari a tsakiyar watan Afrilu sai an samu karin gawawwaki, inda yanzu aka samu 133.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ana zargin shugaban cocin Good News International, Pastor Paul Mackenzie mai shekara 50 da sanya mabiyansa azumi har su mutu, ko su kashe kansu a dalilin hudubar da ya yi musu cewa duniya za ta tashi ranar 15 ga watan Afirilun da ya gabata.

 Ya gaya musu cewa idan suka mutu za su shiga aljanna inda za su hadu da Yesu Almasihu.

Mutanen da aka gano sun mutu ko dai a dalilin azumin da ya kai su ga yunwa har suka mutu ko kuma an shake su ko kuma sun mutu a dalilin buga musu wani abu.

Kungiyar agaji ta Red Cross a kasar ta Kenya ta ce har yanzu akwai mutane 566 da ba a san inda suke ba.

Yayin da mai binciken gawawwaki na gwamnatin kasar ya ce ko dai gawawwakin sarai suke ba a cire wani sashe na jikinsu ba, ko kuma wasu sassan nasu sun fara rubewa, binciken ‘yan sanda ya nuna sabanin hakan.

An gano cewa an ciccire sassan jikin wasu, wanda hakan ke nuna yuwuwar an yi amfani da sassan jikin mutanen.

Ministan tsaro na Kenya ya ce wannan lamari wani mugun laifi ne da aka tsar shi sosai, kuma aikin tono gawawwakin zai dauki lokaci fiye da yadda aka yi tsammani.

A halin da ake ciki kuma an rantsar da wata hukumar bincike ta musamman a babban birnin kasar Nairobi, da kuma wani kwamiti na musamman da na sanya ido a kan harkokin addini domin su gudanar da bincike a kan lamarin.

Masu binciken laifuka a Kenya sun tono karin gawarwaki 21 bayan kaddamar da sabon bincike kan lamarin.

Ministan cikin gida na Kenya Kithure Kindiki ya ce su na binciken ko an yanke gabobin wasu gawawwakin don safarar gabobi.

An dakatar da tono gawawwakin saboda rashin kyawun yanayi a dajin na Shakahola.

An fara tuhumar faston tare da wasu mutanen 14 kan laifukan ta’addanci da dora mutane kan tsattsaurar akida.

Faston
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.