ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Faston

Shugaba cocin nan na Kenya da ake zargi da laifin tilasta wa mabiyansa azumin mutuwa don haduwa da Yesu Almasihu ya sake bayyana a gaban kotu ranar Larabar nan, bayan gurfana da ya yi a ranar Talata.

Hukumomi na gudanar da bincike kan yiwuwar cewa an yi amfani da sassan jikin mutanen da suka mutun.

  • Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo
  • Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Binciken ‘yan sanda ya nuna yadda aka gano karin wasu gawawwakin da aka cire sassan jikinsu.

ADVERTISEMENT

 Wannan ya sa ake ganin da alama an yi amfani da sassan jikin gawawwakin mabiyan na Cocin Good News International, da aka gano a dajin Shakahola na kasar ta Kenya.

Kusan a kullum aka ci gaba da binciken da ake yi tun da aka fara gano wannan al’amari a tsakiyar watan Afrilu sai an samu karin gawawwaki, inda yanzu aka samu 133.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ana zargin shugaban cocin Good News International, Pastor Paul Mackenzie mai shekara 50 da sanya mabiyansa azumi har su mutu, ko su kashe kansu a dalilin hudubar da ya yi musu cewa duniya za ta tashi ranar 15 ga watan Afirilun da ya gabata.

 Ya gaya musu cewa idan suka mutu za su shiga aljanna inda za su hadu da Yesu Almasihu.

Mutanen da aka gano sun mutu ko dai a dalilin azumin da ya kai su ga yunwa har suka mutu ko kuma an shake su ko kuma sun mutu a dalilin buga musu wani abu.

Kungiyar agaji ta Red Cross a kasar ta Kenya ta ce har yanzu akwai mutane 566 da ba a san inda suke ba.

Yayin da mai binciken gawawwaki na gwamnatin kasar ya ce ko dai gawawwakin sarai suke ba a cire wani sashe na jikinsu ba, ko kuma wasu sassan nasu sun fara rubewa, binciken ‘yan sanda ya nuna sabanin hakan.

An gano cewa an ciccire sassan jikin wasu, wanda hakan ke nuna yuwuwar an yi amfani da sassan jikin mutanen.

Ministan tsaro na Kenya ya ce wannan lamari wani mugun laifi ne da aka tsar shi sosai, kuma aikin tono gawawwakin zai dauki lokaci fiye da yadda aka yi tsammani.

A halin da ake ciki kuma an rantsar da wata hukumar bincike ta musamman a babban birnin kasar Nairobi, da kuma wani kwamiti na musamman da na sanya ido a kan harkokin addini domin su gudanar da bincike a kan lamarin.

Masu binciken laifuka a Kenya sun tono karin gawarwaki 21 bayan kaddamar da sabon bincike kan lamarin.

Ministan cikin gida na Kenya Kithure Kindiki ya ce su na binciken ko an yanke gabobin wasu gawawwakin don safarar gabobi.

An dakatar da tono gawawwakin saboda rashin kyawun yanayi a dajin na Shakahola.

An fara tuhumar faston tare da wasu mutanen 14 kan laifukan ta’addanci da dora mutane kan tsattsaurar akida.

Faston
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.