• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

by Khalid Idris Doya
11 months ago
Gombe

Gwamna Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aza tubalin gina katafaren ginin Majalisar Dokoki da Babbar Kotun Jiha a wani bangare na gina cibiyoyin rukunan gwamnati 3 wanda zai kunshi bangaren zartarwa, da sashin majalisa da kuma na shari’a.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa ya bayyana kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawan yanayin aiki ga dukkan bangarorin gwamnati, don ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

Gwamnan ya bayyana cewa an ba da kwangilar gina babbar kotun jihar ne kan kudi naira biliyan 14 da miliyan 900, yayin da ginin majalisar zai lakume naira biliyan 14. da miliyan 5.

Ya yi amfani da wannar dama wajen bayyana aniyarsa ta maida tsohuwar Majalisar Dokoki da Babbar Kotun jihar zuwa asibiti da kwalejin ‘yan mata, don amfanin al’ummar yankin da kewaye.

Da yake bayyana aikin a matsayin wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na cike gibin ababen more rayuwa, Inuwa ya ce, “Tun da aka kirkiro ta shekaru 28 da suka gabata, Jihar Gombe ba ta taba ganin irin wannan aiki ba don samar da yanayin aiki da ya dace ga shugabanni da ma’aikatan gwamnati a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

“Ta hanyar samar musu da wuraren aiki na zamani kamar ko’ina a duniya, muna kara tabbatar da aniya da jajircewarmu na karfafa tsarin gudanar da mulki da ke tabbatar da dimokuradiyya da ci gaban al’umma.

“Tare da wadannan ayyuka, muna fatan bude wani sabon babi da zai kara karfafa alaka da bai wa kowane rukunin gwamnati damar gudanar da ayyukansa yadda ya kamata.

“Wadannan ayyuka ba kawai gine-gine ne na zahiri ba, ginshiki ne na samun ci gaba mai dorewa, inda jagoranci da dimokuradiyya za su karfafa, kuma kowane dan kasa ya samu damar ci gaba yadda ya kamata,” in ji shi.

Gwamnan ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartaswa da sauran bangarorin gwamnati, wanda ya ce ya taimaka wajen cimma nasarorin da gwamnatin mai ci take samu.

Shi ma kwararren mai sanya ido kan aikin daga kamfanin Artec Practice Limited, Arc. Oni Oluseyi, ya ce aikin babbar kotun jihar gini ne na zamani wadda ya kunshi dakunan shari’a 12 masu iya daukar mutane 60, da dakin taro, da ofisoshin alkalai da sauran manyan jami’an shari’a, da dakin karatu na zamani (E-library) da kuma dakin ganawa da manema labarai da dai sauran wurare.

Dangane da ginin majalisar dokokin jihar kuwa, kwararren ya ce an tsara ginin ne zuwa bangarori biyu da suka kunshi zauren majalisa, da ofisoshin kakakin majalisa, da na mataimakinsa da sauran mambobin majalisar, da dakin karatu, da na taro, da wuraren liyafa da dakunan taro, da asibiti da zauren ganawa da manema labarai da dai sauransu.

Manajojin Daraktocin kamfanonin gine-ginen da aka bai wa kwangilolin, Kamfanin Datum Construction, Daher Kaworma da takwaransa na Kamfanin GMC George Maroum, sun tabbatarwa gwamna da al’ummar jihar cewa za su gudanar da ayyuka masu inganci da nagarta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

katsina
Labarai

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kama Barayin Shanu 7 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.