ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Aza Tubalin Gina Majalisar Dokoki Da Babbar Kotun Jiha Na Zamani

by Khalid Idris Doya
12 months ago
Gombe

Gwamna Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aza tubalin gina katafaren ginin Majalisar Dokoki da Babbar Kotun Jiha a wani bangare na gina cibiyoyin rukunan gwamnati 3 wanda zai kunshi bangaren zartarwa, da sashin majalisa da kuma na shari’a.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa ya bayyana kudirin gwamnatinsa na samar da kyakkyawan yanayin aiki ga dukkan bangarorin gwamnati, don ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

Gwamnan ya bayyana cewa an ba da kwangilar gina babbar kotun jihar ne kan kudi naira biliyan 14 da miliyan 900, yayin da ginin majalisar zai lakume naira biliyan 14. da miliyan 5.

ADVERTISEMENT

Ya yi amfani da wannar dama wajen bayyana aniyarsa ta maida tsohuwar Majalisar Dokoki da Babbar Kotun jihar zuwa asibiti da kwalejin ‘yan mata, don amfanin al’ummar yankin da kewaye.

Da yake bayyana aikin a matsayin wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na cike gibin ababen more rayuwa, Inuwa ya ce, “Tun da aka kirkiro ta shekaru 28 da suka gabata, Jihar Gombe ba ta taba ganin irin wannan aiki ba don samar da yanayin aiki da ya dace ga shugabanni da ma’aikatan gwamnati a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

“Ta hanyar samar musu da wuraren aiki na zamani kamar ko’ina a duniya, muna kara tabbatar da aniya da jajircewarmu na karfafa tsarin gudanar da mulki da ke tabbatar da dimokuradiyya da ci gaban al’umma.

“Tare da wadannan ayyuka, muna fatan bude wani sabon babi da zai kara karfafa alaka da bai wa kowane rukunin gwamnati damar gudanar da ayyukansa yadda ya kamata.

“Wadannan ayyuka ba kawai gine-gine ne na zahiri ba, ginshiki ne na samun ci gaba mai dorewa, inda jagoranci da dimokuradiyya za su karfafa, kuma kowane dan kasa ya samu damar ci gaba yadda ya kamata,” in ji shi.

Gwamnan ya yaba da kyakkyawar alakar aiki da ke tsakanin bangaren zartaswa da sauran bangarorin gwamnati, wanda ya ce ya taimaka wajen cimma nasarorin da gwamnatin mai ci take samu.

Shi ma kwararren mai sanya ido kan aikin daga kamfanin Artec Practice Limited, Arc. Oni Oluseyi, ya ce aikin babbar kotun jihar gini ne na zamani wadda ya kunshi dakunan shari’a 12 masu iya daukar mutane 60, da dakin taro, da ofisoshin alkalai da sauran manyan jami’an shari’a, da dakin karatu na zamani (E-library) da kuma dakin ganawa da manema labarai da dai sauran wurare.

Dangane da ginin majalisar dokokin jihar kuwa, kwararren ya ce an tsara ginin ne zuwa bangarori biyu da suka kunshi zauren majalisa, da ofisoshin kakakin majalisa, da na mataimakinsa da sauran mambobin majalisar, da dakin karatu, da na taro, da wuraren liyafa da dakunan taro, da asibiti da zauren ganawa da manema labarai da dai sauransu.

Manajojin Daraktocin kamfanonin gine-ginen da aka bai wa kwangilolin, Kamfanin Datum Construction, Daher Kaworma da takwaransa na Kamfanin GMC George Maroum, sun tabbatarwa gwamna da al’ummar jihar cewa za su gudanar da ayyuka masu inganci da nagarta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Labarai

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
Next Post
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

'Yansanda Sun Kama Barayin Shanu 7 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.