ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

Kasashen Afirka sun dade suna kasancewa masu samar da danyun kayayyaki da ma’adinai, a bisa tsarin samar da kayayyaki na duniya. Sai dai lokaci ya yi da za a kawo sauye-sauye.

 

A kwanan nan, a birnin Beijing na kasar Sin, ana gudanar da bikin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na duniya a kasar Sin, wato CISCE, a karo na biyu, wanda ya kasance wani muhimmin dandalin da kasar Sin ta kafa don karfafa hadin kan kasashe daban daban, ta fuskar tsare-tsaren masana’antu da na samar da kayayyaki. Kana bikin na da ma’anar musamman ga kasar Sin, da kasashen dake nahiyar Afirka.

ADVERTISEMENT
  • Ɗansanda Ya Gamu Da Ajalinsa Bayan Fasa Tukunyar Miya A Adamawa
  • Xi Ya Bukaci A Aiwatar Da Kudurin Kwamitin Sulhun MDD Kan Batun Palastinu

Wani babban dalilin da ya sa kasar Sin kafa bikin CISCE, shi ne domin tinkarar matakan da kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya suka dauka, na kin dunkulewar tattalin arzikin duniya waje guda. Wadannan kasashe suna neman rage tasirin kasar Sin a tsare-tsaren masana’antu da na samar da kayayyaki na duniya, ta yadda su da kansu za su sake hawa kujerar jagorancin tattalin arzikin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Hakika kasashen Afirka sun fahimci nau’in matakan kasar Amurka da na kawayenta sosai, saboda matakai ne na mai da wani saniyar ware, wadanda suka yi kama da matakan da ‘yan mulki mallaka suka dauka a nahiyar Afirka, kamarsu nuna bambancin launin fata, da tilasta wa nahiyar Afirka kasancewa a matsayin mai samar da danyun kayayyaki, da zama babbar kasuwar da ake sayar da kayayyakin masana’antu. A ganin Amurka da kawayenta, ta hanyar hana sauran kasashe tasowa, za su iya kare fifikonsu har abada. Amma dai kamar yadda aka kawar da manufar bambancin launin fata, duk wata manufar da aka tsara, in dai ba ta da adalci, to, tabbas ne za a kawo karshenta a wata rana.

 

Ko da yake tun daga lokacin mulkin mallaka, an dade ana amfani da tsohon tsarin tattalin arziki wajen danne kasashen Afirka, amma yanzu an fara samun sauyawar yanayi. Bisa wani rahoton da taron ciniki da batun ci gaba na Majalisar Dinkin Duniya, wato UNCTAD a takaice, ya gabatar, an ce don neman tinkarar matakan kin dunkulewar tattalin arzikin duniya, wasu sabbin masana’antu, irinsu na hada motoci, da kayayyakin latironi, da makamashin ake iya sabuntawa, da magunguna, da kayayyakin aikin jinya, da dai sauransu, suna kokarin raba bangarori masu samar musu da kayayyaki a wurare daban-daban, don magance yiwuwar katsewar hanyar samun kayan da ake bukata. Wannan yanayi, a cewar UNCTAD, na samar da damammaki ga kasashen Afirka, don su taka rawar gani a tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya.

 

An ce, kasashen Afirka za su iya amfani da fifikonsu na samun dimbin al’umma, da ma’adinai masu muhimmanci, wajen zama kasashen dake samar da sassan kayayyakin da ake bukata a wasu sabbin sana’o’i. Sai dai kafin su iya cimma wannan buri, ya kamata kasashen Afirka su inganta kayayyakinsu na more rayuwa, da horar da ma’aikata, da neman jari da fasahohin da suke bukata. Kana a wadannan fannoni, kasar Sin ta dade tana hadin gwiwa da kasashen Afirka, cikin wani yanayi mai gamsarwa.

 

Hakika duk wani tsohon tsari, idan aka ga an kawo karshensa a wata rana, tabbas domin yana haifar da rashin jin dadi a zukatan mutanen duniya ne. A nan za mu iya ba da misalin tashar jiragen ruwa ta Chankay ta kasar Peru, wadda aka gina da dalar Amurka biliyan 3.5, a hadin gwiwar kasashen Peru da Sin, tare da burin inganta aikin jigilar kayayyaki cikin tekun Fasifik. Bayan da aka kaddamar da tashar a kwanan baya, shugabannin kasashen Latin Amurka da dama sun bayyana farin cikinsu da kakkyawan fatan da aka sanya a aikin. Amma a nata bangare, gwamnatin Trump mai jiran gado ta kasar Amurka ta yi gargadin cewa, za ta karbi harajin kwastam da ya kai kaso 60%, kan dukkan kayayyakin da aka kai su kasar Amurka da aka bi ta tashar Chancay da su. Dalilin da ya sa take son daukar matakin kawai shi ne, Amurka ta ce, nasarar da aka samu a tashar Chancay za ta iya karfafa gwiwar sauran kasashen dake Latin Amurka su karfafa zumuntar dake tsakaninsu da kasar Sin.

 

Ta wannan misali za mu iya ganin yadda kasar Sin take kokarin hadin gwiwa da sauran kasashe, da tabbatar da moriyar juna, yayin da kasar Amurka ke neman saka takunkumi da yanke danyen hukunci a kan kasashe da dama, don kare moriyar kanta. Wannan bambanci a sarari ya nuna, shin wane bangare ne yake da adalci. (Bello Wang)

 

 

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.