• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya kafa doka mai lamba 8 ta 2024, da nufin tsaurara matakan sanya ido da kuma daidaita harkokin hakar ma’adanai a fadin Jihar Gombe don kare al’ummomin da ake hako ma’adanan a cikinsu daga cin zarafi da kuma kare muhalli.

Dokar wacce ta fara aiki nan take, za ta magance kalubale daban-daban da hakar ma’adanai ke haifarwa, wadanda suka hada da lalata muhalli da haddasa matsalolin tsaro da cin zarafin al’ummomin da ake hako ma’adanan a cikinsu.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

Muhimman abubuwan da suka shafi dokar sun hada da kafa kwamitin sanya ido kan ayyukan hako ma’adanai (MAMC), wanda kwamishinan makamashi da ma’adinai ke jagoranta.

Kwamitin ya kunshi wakilai daga ma’aikatu da hukumomin tsaro daban-daban, da Hukumar Zamanantar da Harkokin Filaye ta Jihar Gombe (GOGIS). Kwamitin yana da alhakin kula da duk wasu harkokin hakar ma’adinai a jihar, da tabbatar da bin dokoki da kuma hada kai da hukumomin gwamnatin tarayya don rage matsalolin muhalli.

Wani muhimmin al’amari na dokar shi ne, yadda ta bukaci duk kamfanonin hako ma’adanai su mika takardar yarjejeniyar amincewa da ta ci gaban al’ummar da za a hako ma’adanan a yankinsu zuwa ga ma’aikatar shari’a ta jihar ta hannun ma’aikatar makamashi da ma’adinai don tantancewa kafin fara duk wani aiki na hako ma’adanan.

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar Gombe, Ismaila Uba Misilli a wata sanarwar da ya fitar, ya ce, wannan matakin zai tabbatar da ana gudanar da ayyukan hakar ma’adanan daidai da muradun al’ummomin da ke wurin da kuma tabbatar da cewa duk yarjeniyoyin sun samu sahalewar doka.

Haka kuma, dokar ta ba da umarnin cewa duk ma’aikatan kamfanonin hako ma’adinai da suka zo Jihar Gombe, dole ne kwamitin na MAMC ya tantancesu don tabbatar da su ko suna da takardun izinin zama a Nijeriya, da ma matsayinsu a fuskar shari’a.

Haka kuma dokar ta zayyano irin rawar da hukumar tattara kudaden shiga ta Jihar Gombe (GIRS) da kananan hukumomi za su taka wajen karbar haraji da kudaden shiga daga kamfanonin hako ma’adanai a jihar.

Kwamitin na MAMC tare da hadin gwiwar wadannan hukumomi ne ke da alhakin tabbatar da bin umarnin bincike da gurfanar da duk wadda aka samu da karya dokar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeMa’adanai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Karyewar Darajar Naira Da Cire Tallafin Mai Suka Durkusar Da Masana’antun Kasar Nan

Next Post

Gwamnati Ta Karyata Shirin Karin Harajin VAT

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

21 hours ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

22 hours ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

23 hours ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Gwamnati Ta Karyata Shirin Karin Harajin VAT

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.