ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Kafa Doka Kan Hakar Ma’adanai Don Kare Muhalli

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya kafa doka mai lamba 8 ta 2024, da nufin tsaurara matakan sanya ido da kuma daidaita harkokin hakar ma’adanai a fadin Jihar Gombe don kare al’ummomin da ake hako ma’adanan a cikinsu daga cin zarafi da kuma kare muhalli.

Dokar wacce ta fara aiki nan take, za ta magance kalubale daban-daban da hakar ma’adanai ke haifarwa, wadanda suka hada da lalata muhalli da haddasa matsalolin tsaro da cin zarafin al’ummomin da ake hako ma’adanan a cikinsu.

  • Sin Ta Kulla Yarjejeniyar Tsarin Kafa Huldar Abota Ta Raya Tattalin Arziki Cikin Hadin Gwiwa Tsakaninta Da Kasashen Afirka 22.
  • Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

Muhimman abubuwan da suka shafi dokar sun hada da kafa kwamitin sanya ido kan ayyukan hako ma’adanai (MAMC), wanda kwamishinan makamashi da ma’adinai ke jagoranta.

ADVERTISEMENT

Kwamitin ya kunshi wakilai daga ma’aikatu da hukumomin tsaro daban-daban, da Hukumar Zamanantar da Harkokin Filaye ta Jihar Gombe (GOGIS). Kwamitin yana da alhakin kula da duk wasu harkokin hakar ma’adinai a jihar, da tabbatar da bin dokoki da kuma hada kai da hukumomin gwamnatin tarayya don rage matsalolin muhalli.

Wani muhimmin al’amari na dokar shi ne, yadda ta bukaci duk kamfanonin hako ma’adanai su mika takardar yarjejeniyar amincewa da ta ci gaban al’ummar da za a hako ma’adanan a yankinsu zuwa ga ma’aikatar shari’a ta jihar ta hannun ma’aikatar makamashi da ma’adinai don tantancewa kafin fara duk wani aiki na hako ma’adanan.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Babban Daraktan Yada Labarun Gwamnan Jihar Gombe, Ismaila Uba Misilli a wata sanarwar da ya fitar, ya ce, wannan matakin zai tabbatar da ana gudanar da ayyukan hakar ma’adanan daidai da muradun al’ummomin da ke wurin da kuma tabbatar da cewa duk yarjeniyoyin sun samu sahalewar doka.

Haka kuma, dokar ta ba da umarnin cewa duk ma’aikatan kamfanonin hako ma’adinai da suka zo Jihar Gombe, dole ne kwamitin na MAMC ya tantancesu don tabbatar da su ko suna da takardun izinin zama a Nijeriya, da ma matsayinsu a fuskar shari’a.

Haka kuma dokar ta zayyano irin rawar da hukumar tattara kudaden shiga ta Jihar Gombe (GIRS) da kananan hukumomi za su taka wajen karbar haraji da kudaden shiga daga kamfanonin hako ma’adanai a jihar.

Kwamitin na MAMC tare da hadin gwiwar wadannan hukumomi ne ke da alhakin tabbatar da bin umarnin bincike da gurfanar da duk wadda aka samu da karya dokar.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Next Post
Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Gwamnati Ta Karyata Shirin Karin Harajin VAT

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.