• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kakkausar suka da Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wani matashi dan shekaru 45, Ahmed Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, inda wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka kai masa hari tare da kashe shi a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe.

Mummunan lamarin ya faru ne a daren ranar Lahadin da ta gabata, inda aka cakka wa marigayin wuka, kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa a asibitin kwararru na Gombe, kamar yadda rahotannin tsaro suka tabbatar.

  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

Da yake tsokaci kan lamarin, Gwamna Yahaya ya nuna bacin rai da alhininsa, inda ya bayyana kisan a matsayin rashin hankali, kuma abin da sam ba za a lamunta ba.

Ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da sake dawowar aika-aikar ‘yan kalare da ‘yan daba a Gombe ba, kamar yadda kakakinsa Ismala Uba Misilli ya fitar ta cikin wata sanarwa.

“Wannan mummunan aika-aika ne kai tsaye ga zaman lafiya da tsaron al’ummarmu, a sani, tashin hankali ba shi da gurbi a Jihar Gombe, kuma za mu sanya kafar wando daya da duk wanda aka kama yana tada zaune tsaye,” in ji gwamnan.

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.

“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.

“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.

“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”

Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

28 minutes ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

1 hour ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

10 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

11 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

12 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

13 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.