ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kaduna Ya Amince Da Bayar Da Alawus Ga Malamai Da Ke Karantarwa A Yankunan Karkara

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 days ago
Kaduna

A wani muhimmin mataki na ƙarfafa fannin ilimi da kuma girmama jajircewar aiki , Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da ingantattun sharuddan aiki ga malamai a faɗin jihar.

Gwamnan yace daga ranar 1 ga Agusta, 2025, an ƙara shekarun ritaya ga malamai daga shekara 60 zuwa 65, yayin da adadin shekarun hidima kuma ya ƙaru daga shekara 35 zuwa 40.

  • Sin Za Ta Fadada Bude Kofarta A Fannin Ba Da Hidima
  • Mujallar “Science”: Kasar Sin Tana Jagorantar Sauyin Salon Makamashi A Duniya

Bugu da ƙari, malamai da aka tura zuwa yankunan karkara da wuraren da ke da wahalar isa za su rika karɓar alawus na musamman na aikin karkara.

ADVERTISEMENT

Wannan amincewar ta yi daidai da Dokar Daidaita Shekarun ritaya ga Malamai a Nijeriya ta 2022, wadda Majalisar Tarayya ta kafa, wacce ta keɓe malamai daga ƙa’idar ritayar ma’aikatan gwamnati ta shekara 60 ko shekaru 35 na hidima, bisa la’akari da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ci gaban ƙasa.

A wata sanarwa da wamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kaduna, Alhaji Ahmed Maiyaki, ya rabawa manema labarai ya ce wannan mataki yana nuna ƙudurin Gwamna Uba Sani na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da fannin ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Ya bayyana cewa Gwamnan na ganin gogaggun malamai a matsayin ginshiƙi wajen samar da ingantaccen ilimi da ci gaba da kyakkyawan sakamakon koyo a duk faɗin jihar.

A cewarsa “Wannan manufa an tsara ta ne domin girmama shekaru na sadaukar da kai, riƙe ƙwarewa mai matuƙar amfani a cikin ajujuwanmu, da kuma ƙarfafa ƙwazo da aiki tukuru domin amfanin ’ya’yanmu da makomar Jihar Kaduna,” in ji Maiyaki.

Hakazalika, a wata takardada aka fita daga Ofishin Gwamna mai ɗauke da wannan amincewa, wadda Babbar Sakatariya ,Felicia I. Makama, ta sanya wa hannu, tare da umartar dukkan hukumomin da abin ya shafa da su bi umarnin.

Takardar ta ƙara da cewa Hukumar Kula da Ayyukan Gwamnatin Jihar za ta fitar da cikakkun ƙa’idojin aiwatarwa nan gaba kaɗan.

Gwamna Sani ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa wannan manufa za ta ƙara wa malamai ƙwarin gwiwa, ta inganta riƙon ma’aikata, tare da ɗaga matakin ilimi sosai a faɗin Jihar Kaduna, a matsayin wani ɓangare na ƙudurin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin gwamnati da zuba jari a ci gaban ɗan Adam.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.