ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kaduna Ya Amince Da Bayar Da Alawus Ga Malamai Da Ke Karantarwa A Yankunan Karkara

by Shehu Yahaya and Sulaiman
8 months ago
Kaduna

A wani muhimmin mataki na ƙarfafa fannin ilimi da kuma girmama jajircewar aiki , Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da ingantattun sharuddan aiki ga malamai a faɗin jihar.

Gwamnan yace daga ranar 1 ga Agusta, 2025, an ƙara shekarun ritaya ga malamai daga shekara 60 zuwa 65, yayin da adadin shekarun hidima kuma ya ƙaru daga shekara 35 zuwa 40.

  • Sin Za Ta Fadada Bude Kofarta A Fannin Ba Da Hidima
  • Mujallar “Science”: Kasar Sin Tana Jagorantar Sauyin Salon Makamashi A Duniya

Bugu da ƙari, malamai da aka tura zuwa yankunan karkara da wuraren da ke da wahalar isa za su rika karɓar alawus na musamman na aikin karkara.

ADVERTISEMENT

Wannan amincewar ta yi daidai da Dokar Daidaita Shekarun ritaya ga Malamai a Nijeriya ta 2022, wadda Majalisar Tarayya ta kafa, wacce ta keɓe malamai daga ƙa’idar ritayar ma’aikatan gwamnati ta shekara 60 ko shekaru 35 na hidima, bisa la’akari da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ci gaban ƙasa.

A wata sanarwa da wamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kaduna, Alhaji Ahmed Maiyaki, ya rabawa manema labarai ya ce wannan mataki yana nuna ƙudurin Gwamna Uba Sani na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da fannin ilimi.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

Ya bayyana cewa Gwamnan na ganin gogaggun malamai a matsayin ginshiƙi wajen samar da ingantaccen ilimi da ci gaba da kyakkyawan sakamakon koyo a duk faɗin jihar.

A cewarsa “Wannan manufa an tsara ta ne domin girmama shekaru na sadaukar da kai, riƙe ƙwarewa mai matuƙar amfani a cikin ajujuwanmu, da kuma ƙarfafa ƙwazo da aiki tukuru domin amfanin ’ya’yanmu da makomar Jihar Kaduna,” in ji Maiyaki.

Hakazalika, a wata takardada aka fita daga Ofishin Gwamna mai ɗauke da wannan amincewa, wadda Babbar Sakatariya ,Felicia I. Makama, ta sanya wa hannu, tare da umartar dukkan hukumomin da abin ya shafa da su bi umarnin.

Takardar ta ƙara da cewa Hukumar Kula da Ayyukan Gwamnatin Jihar za ta fitar da cikakkun ƙa’idojin aiwatarwa nan gaba kaɗan.

Gwamna Sani ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa wannan manufa za ta ƙara wa malamai ƙwarin gwiwa, ta inganta riƙon ma’aikata, tare da ɗaga matakin ilimi sosai a faɗin Jihar Kaduna, a matsayin wani ɓangare na ƙudurin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin gwamnati da zuba jari a ci gaban ɗan Adam.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    2027: Ƙungiyar Musulman Kudancin Kaduna Ta Yi Gargaɗi Kan Siyasantar Da Addini
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Jinin Waɗanda Aka Kashe Wajen Haƙar Ma’adanai a Birnin Gwari Ba Zai Tafi Banza Ba – Hon. Bashir Zubairu
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Kaduna

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Kaduna

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.