ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kaduna Ya Amince Da Bayar Da Alawus Ga Malamai Da Ke Karantarwa A Yankunan Karkara

by Shehu Yahaya and Sulaiman
6 months ago
Kaduna

A wani muhimmin mataki na ƙarfafa fannin ilimi da kuma girmama jajircewar aiki , Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da ingantattun sharuddan aiki ga malamai a faɗin jihar.

Gwamnan yace daga ranar 1 ga Agusta, 2025, an ƙara shekarun ritaya ga malamai daga shekara 60 zuwa 65, yayin da adadin shekarun hidima kuma ya ƙaru daga shekara 35 zuwa 40.

  • Sin Za Ta Fadada Bude Kofarta A Fannin Ba Da Hidima
  • Mujallar “Science”: Kasar Sin Tana Jagorantar Sauyin Salon Makamashi A Duniya

Bugu da ƙari, malamai da aka tura zuwa yankunan karkara da wuraren da ke da wahalar isa za su rika karɓar alawus na musamman na aikin karkara.

ADVERTISEMENT

Wannan amincewar ta yi daidai da Dokar Daidaita Shekarun ritaya ga Malamai a Nijeriya ta 2022, wadda Majalisar Tarayya ta kafa, wacce ta keɓe malamai daga ƙa’idar ritayar ma’aikatan gwamnati ta shekara 60 ko shekaru 35 na hidima, bisa la’akari da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ci gaban ƙasa.

A wata sanarwa da wamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kaduna, Alhaji Ahmed Maiyaki, ya rabawa manema labarai ya ce wannan mataki yana nuna ƙudurin Gwamna Uba Sani na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da fannin ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ya bayyana cewa Gwamnan na ganin gogaggun malamai a matsayin ginshiƙi wajen samar da ingantaccen ilimi da ci gaba da kyakkyawan sakamakon koyo a duk faɗin jihar.

A cewarsa “Wannan manufa an tsara ta ne domin girmama shekaru na sadaukar da kai, riƙe ƙwarewa mai matuƙar amfani a cikin ajujuwanmu, da kuma ƙarfafa ƙwazo da aiki tukuru domin amfanin ’ya’yanmu da makomar Jihar Kaduna,” in ji Maiyaki.

Hakazalika, a wata takardada aka fita daga Ofishin Gwamna mai ɗauke da wannan amincewa, wadda Babbar Sakatariya ,Felicia I. Makama, ta sanya wa hannu, tare da umartar dukkan hukumomin da abin ya shafa da su bi umarnin.

Takardar ta ƙara da cewa Hukumar Kula da Ayyukan Gwamnatin Jihar za ta fitar da cikakkun ƙa’idojin aiwatarwa nan gaba kaɗan.

Gwamna Sani ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa wannan manufa za ta ƙara wa malamai ƙwarin gwiwa, ta inganta riƙon ma’aikata, tare da ɗaga matakin ilimi sosai a faɗin Jihar Kaduna, a matsayin wani ɓangare na ƙudurin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin gwamnati da zuba jari a ci gaban ɗan Adam.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

Wakilin Sin A MDD Ya Ce Dole Ne Japan Ta Zurfafa Karatun Baya Game Da Laifukanta A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.