• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Nasarawa Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Dan Takarar Gwamna Na PDP

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
An Sake Zabar Gwamna Sule A Matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa A Karo Na 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke Lafiya, Jihar Nasarawa, na dakon yanke hukunci kan karar da ke kalubalantar sakamakon zaben 2023 a jihar.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Mista David Ombugadu, yana kalubalantar ayyana Gwamna Abdullahi Sule na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a 2023.

  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Rushe Gine-ginen Da Aka Yi A Kan Magudanar Ruwa
  • Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

An dai shirya zaman kotun a ranar Alhamis don kammala karɓar hujjoji da jawaban lauyoyi na ƙarshe daga ɓangaren mai shigar da kara da jam’iyya da kuma wanda ake kara ko tuhuma.

Alkalin da ke jagorantar zaman shari’ar, Mai shari’a Ezekiel Ajayi, ya dage zaman kotun bayan lauyoyin masu kara da wadanda ake kara sun amince da bukatunsu na karshe a rubuce.
Don haka mai shari’ar ya ce kotun za ta tuntubi bangarorin ta hanyar lauyoyinsu kan ranar da za a yanke hukunci.

Tun da farko, Kanu Agabi (SAN), jagoran masu shigar da kara ya shaida wa kotun cewa ya amince da duk hujjojin da ke cikin rubutattun bukatun da aka gabatarwa kotu.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Lauyan mai kara ya bukaci kotun da ta soke zaben Gwamnan Jihar Nasarawa saboda rashin bin dokar zabe tare da bayyana dan takarar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben.

Agabi ya kuma bayyana cewa babu wata alaka tsakanin kuri’u a na’urar IREV da sakamakon karshe da aka bayyana.

Lauyan mai shigar da kara ya ce dan takarar PDP ne ya fi yawan kuri’un da aka kada a zaben, bisa ga bayanan da ke cikin IREV da bayanan na’urorin BVAS da aka yi amfani da su a rumfunan zabe daban-daban.

A nasu bangaren, lauyoyin hukumar zabe ta INEC, APC, da Gwamna Sule, Mista Isiaka Dikko (SAN), Hassan Liman (SAN) da Messrs Wole Olanikpekun (SAN), sun rubuta bukatarsu ta karshe a rubuce tare da yin kira ga kotun da ta yi watsi da karar don rashin cancantar saurarensu.

Lauyan jam’iyyar APC, Olanikpekun ya kuma yi zargin cewa mai shigar da karar ya yi watsi da na’urar BVAS da kuma bayanan IREV a kotun ba tare da nuna abin da ke kunshe a cikin bayanan ba.

Ya ce mai shigar da karar ya gabatar da bayanan ne kawai a cikin na’urar IREV da BVAS ga kotun ba tare da nuna su ɓaro-ɓaro a kotun ba.

Don haka ya ce wanda ya shigar da karar ya kasa tabbatar da komai don haka ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi SuleGwamnan NasarawaKotuKotun Sauraren kararrakin zaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Venezuela Sun Inganta Dankon Zumunci A Tsakaninsu

Next Post

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

Related

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

12 minutes ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

6 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

6 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

7 hours ago
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa
Labarai

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

9 hours ago
Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 
Manyan Labarai

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

11 hours ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

June 21, 2025
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

June 21, 2025
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.