• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Nasarawa Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Dan Takarar Gwamna Na PDP

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
An Sake Zabar Gwamna Sule A Matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa A Karo Na 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke Lafiya, Jihar Nasarawa, na dakon yanke hukunci kan karar da ke kalubalantar sakamakon zaben 2023 a jihar.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Mista David Ombugadu, yana kalubalantar ayyana Gwamna Abdullahi Sule na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a 2023.

  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Rushe Gine-ginen Da Aka Yi A Kan Magudanar Ruwa
  • Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

An dai shirya zaman kotun a ranar Alhamis don kammala karɓar hujjoji da jawaban lauyoyi na ƙarshe daga ɓangaren mai shigar da kara da jam’iyya da kuma wanda ake kara ko tuhuma.

Alkalin da ke jagorantar zaman shari’ar, Mai shari’a Ezekiel Ajayi, ya dage zaman kotun bayan lauyoyin masu kara da wadanda ake kara sun amince da bukatunsu na karshe a rubuce.
Don haka mai shari’ar ya ce kotun za ta tuntubi bangarorin ta hanyar lauyoyinsu kan ranar da za a yanke hukunci.

Tun da farko, Kanu Agabi (SAN), jagoran masu shigar da kara ya shaida wa kotun cewa ya amince da duk hujjojin da ke cikin rubutattun bukatun da aka gabatarwa kotu.

Labarai Masu Nasaba

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Lauyan mai kara ya bukaci kotun da ta soke zaben Gwamnan Jihar Nasarawa saboda rashin bin dokar zabe tare da bayyana dan takarar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben.

Agabi ya kuma bayyana cewa babu wata alaka tsakanin kuri’u a na’urar IREV da sakamakon karshe da aka bayyana.

Lauyan mai shigar da kara ya ce dan takarar PDP ne ya fi yawan kuri’un da aka kada a zaben, bisa ga bayanan da ke cikin IREV da bayanan na’urorin BVAS da aka yi amfani da su a rumfunan zabe daban-daban.

A nasu bangaren, lauyoyin hukumar zabe ta INEC, APC, da Gwamna Sule, Mista Isiaka Dikko (SAN), Hassan Liman (SAN) da Messrs Wole Olanikpekun (SAN), sun rubuta bukatarsu ta karshe a rubuce tare da yin kira ga kotun da ta yi watsi da karar don rashin cancantar saurarensu.

Lauyan jam’iyyar APC, Olanikpekun ya kuma yi zargin cewa mai shigar da karar ya yi watsi da na’urar BVAS da kuma bayanan IREV a kotun ba tare da nuna abin da ke kunshe a cikin bayanan ba.

Ya ce mai shigar da karar ya gabatar da bayanan ne kawai a cikin na’urar IREV da BVAS ga kotun ba tare da nuna su ɓaro-ɓaro a kotun ba.

Don haka ya ce wanda ya shigar da karar ya kasa tabbatar da komai don haka ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi SuleGwamnan NasarawaKotuKotun Sauraren kararrakin zaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Venezuela Sun Inganta Dankon Zumunci A Tsakaninsu

Next Post

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

Related

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

16 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

16 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

16 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

18 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

19 hours ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.