ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Nasarawa Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Dan Takarar Gwamna Na PDP

by Abubakar Abba
3 years ago
Kotu

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke Lafiya, Jihar Nasarawa, na dakon yanke hukunci kan karar da ke kalubalantar sakamakon zaben 2023 a jihar.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Mista David Ombugadu, yana kalubalantar ayyana Gwamna Abdullahi Sule na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a 2023.

  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Rushe Gine-ginen Da Aka Yi A Kan Magudanar Ruwa
  • Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

An dai shirya zaman kotun a ranar Alhamis don kammala karɓar hujjoji da jawaban lauyoyi na ƙarshe daga ɓangaren mai shigar da kara da jam’iyya da kuma wanda ake kara ko tuhuma.

ADVERTISEMENT

Alkalin da ke jagorantar zaman shari’ar, Mai shari’a Ezekiel Ajayi, ya dage zaman kotun bayan lauyoyin masu kara da wadanda ake kara sun amince da bukatunsu na karshe a rubuce.
Don haka mai shari’ar ya ce kotun za ta tuntubi bangarorin ta hanyar lauyoyinsu kan ranar da za a yanke hukunci.

Tun da farko, Kanu Agabi (SAN), jagoran masu shigar da kara ya shaida wa kotun cewa ya amince da duk hujjojin da ke cikin rubutattun bukatun da aka gabatarwa kotu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Lauyan mai kara ya bukaci kotun da ta soke zaben Gwamnan Jihar Nasarawa saboda rashin bin dokar zabe tare da bayyana dan takarar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben.

Agabi ya kuma bayyana cewa babu wata alaka tsakanin kuri’u a na’urar IREV da sakamakon karshe da aka bayyana.

Lauyan mai shigar da kara ya ce dan takarar PDP ne ya fi yawan kuri’un da aka kada a zaben, bisa ga bayanan da ke cikin IREV da bayanan na’urorin BVAS da aka yi amfani da su a rumfunan zabe daban-daban.

A nasu bangaren, lauyoyin hukumar zabe ta INEC, APC, da Gwamna Sule, Mista Isiaka Dikko (SAN), Hassan Liman (SAN) da Messrs Wole Olanikpekun (SAN), sun rubuta bukatarsu ta karshe a rubuce tare da yin kira ga kotun da ta yi watsi da karar don rashin cancantar saurarensu.

Lauyan jam’iyyar APC, Olanikpekun ya kuma yi zargin cewa mai shigar da karar ya yi watsi da na’urar BVAS da kuma bayanan IREV a kotun ba tare da nuna abin da ke kunshe a cikin bayanan ba.

Ya ce mai shigar da karar ya gabatar da bayanan ne kawai a cikin na’urar IREV da BVAS ga kotun ba tare da nuna su ɓaro-ɓaro a kotun ba.

Don haka ya ce wanda ya shigar da karar ya kasa tabbatar da komai don haka ya bukaci kotun da ta yi watsi da karar.

Kotu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Shawarar EU Ta Kaddamar Da Binciken Ba Da Rangwame Kan Motocin Sin Masu Amfani Da Wutar Lantarki 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.