• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Rabon Naira Biliyan 11 Na Bunkasa Ilimin Mata A Jihar

byLeadership Hausa
1 year ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da shirin raba maƙudan kuɗaɗe ga Ƙanana da Matsakaitan Makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin Samar da Ilimi da Ƙarfafa ’Ya’ya Mata (AGILE) a jihar.

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnan ya raba wa ’yan kwangilar da aka zaɓa a matsayin Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman takardun fara aiki don ayyukan gyara da kuma inganta makarantu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce aikin na da nufin inganta dukkan makarantu a faɗin jihar.

Ya ƙara da cewa, rabon kuxin shi ne kashi na farko na tallafin inganta ƙananan makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin AGILE.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Da yake gabatar da nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa an zaɓo makarantu 322 domin gudanar da aikin, wanda kuɗinsu ya kai Naira 11,736,000,000.00.

“A yau wani gagarumin ci gaba ne a cikin ƙudirinmu na cika alƙawuran yaƙin neman zaɓe na farfaɗo da harkar ilimi a Jihar Zamfara yayin da muka ƙaddamar da shirin bayar da tallafin Inganta Makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin AGILE.

“Idan za ku iya tunawa cewa mun ayyana dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi, kuma wannan shirin na nuni da ci gaba da shawarar da muka yanke na gyara da kuma inganta ababen more rayuwa a makarantu.

“Saboda haka, wannan taro wani muhimmin mataki ne a cikin tsarin, domin an raba wa ’yan kwangilar da aka zaɓa a matsayin Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman takardun fara aiki don ayyukan gyara da kuma inganta makarantu.

“Wannan mataki ne mai muhimmanci wajen samar da ingantaccen yanayin samun ilimi ga yaranmu.

“A matsayinku na Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman, rawar ku na da muhimmanci wajen tabbatar da cewa kowace naira da aka kashe ta nuna kanta a ci gaban da aka samu a makarantunmu.

Gwamna Lawal ya kuma buƙaci Masu gudanar da ayyuka na musamman ɗin da su bi tsare-tsaren inganta makarantu (SIPS) da ƙa’idoji yadda ya kamata.

“A yunƙurinmu na tabbatar da cewa aikin ya kai matsayin da ake buƙata, mun kafa wata hanya mai ƙarfi don sa ido kan aiwatarwa da kuma tabbatar da bin duk ƙa’idoji da ƙayyadaddun bayanai.

“Ina kuma kira ga tawagar sa ido kan ayyukan da kwamitin gudanarwa na makarantu (SBMC), da sauran jama’a da su kasance cikin shiri da kuma tsunduma cikin wannan aiki. Wannan yunƙurin ba wai kawai na gina makarantu da sabunta su ba ne; ya shafi zuba jari ne a makomar jihar Zamfara.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
An Yi Artabu Tsakanin ‘Yansanda Da Zaunagari-banza A Abuja

Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version