• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Rabon Naira Biliyan 11 Na Bunkasa Ilimin Mata A Jihar

by Leadership Hausa
10 months ago
in Ilimi
0
Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Rabon Naira Biliyan 11 Na Bunkasa Ilimin Mata A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da shirin raba maƙudan kuɗaɗe ga Ƙanana da Matsakaitan Makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin Samar da Ilimi da Ƙarfafa ’Ya’ya Mata (AGILE) a jihar.

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnan ya raba wa ’yan kwangilar da aka zaɓa a matsayin Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman takardun fara aiki don ayyukan gyara da kuma inganta makarantu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce aikin na da nufin inganta dukkan makarantu a faɗin jihar.

Ya ƙara da cewa, rabon kuxin shi ne kashi na farko na tallafin inganta ƙananan makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin AGILE.

zamfara

Labarai Masu Nasaba

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Da yake gabatar da nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa an zaɓo makarantu 322 domin gudanar da aikin, wanda kuɗinsu ya kai Naira 11,736,000,000.00.

“A yau wani gagarumin ci gaba ne a cikin ƙudirinmu na cika alƙawuran yaƙin neman zaɓe na farfaɗo da harkar ilimi a Jihar Zamfara yayin da muka ƙaddamar da shirin bayar da tallafin Inganta Makarantu (SIGS) a ƙarƙashin shirin AGILE.

“Idan za ku iya tunawa cewa mun ayyana dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi, kuma wannan shirin na nuni da ci gaba da shawarar da muka yanke na gyara da kuma inganta ababen more rayuwa a makarantu.

“Saboda haka, wannan taro wani muhimmin mataki ne a cikin tsarin, domin an raba wa ’yan kwangilar da aka zaɓa a matsayin Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman takardun fara aiki don ayyukan gyara da kuma inganta makarantu.

“Wannan mataki ne mai muhimmanci wajen samar da ingantaccen yanayin samun ilimi ga yaranmu.

“A matsayinku na Masu Gudanar da Ayyuka na Musamman, rawar ku na da muhimmanci wajen tabbatar da cewa kowace naira da aka kashe ta nuna kanta a ci gaban da aka samu a makarantunmu.

Gwamna Lawal ya kuma buƙaci Masu gudanar da ayyuka na musamman ɗin da su bi tsare-tsaren inganta makarantu (SIPS) da ƙa’idoji yadda ya kamata.

“A yunƙurinmu na tabbatar da cewa aikin ya kai matsayin da ake buƙata, mun kafa wata hanya mai ƙarfi don sa ido kan aiwatarwa da kuma tabbatar da bin duk ƙa’idoji da ƙayyadaddun bayanai.

“Ina kuma kira ga tawagar sa ido kan ayyukan da kwamitin gudanarwa na makarantu (SBMC), da sauran jama’a da su kasance cikin shiri da kuma tsunduma cikin wannan aiki. Wannan yunƙurin ba wai kawai na gina makarantu da sabunta su ba ne; ya shafi zuba jari ne a makomar jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BunkasaCi GabaGwamna Dauda LawalIlimiMataZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwan Maiduguri Ta Shafi Mutane Sama Da Miliyan 1 – Gwamnati

Next Post

Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

Related

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

3 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

3 days ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

3 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

1 week ago
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
Ilimi

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

2 weeks ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

4 weeks ago
Next Post
An Yi Artabu Tsakanin ‘Yansanda Da Zaunagari-banza A Abuja

Kotu Ta Bada Belin Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Kan Naira Milyan 10 Kowanensu

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.