• English
  • Business News
Thursday, July 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar

Abubuwan Da Suka Wakana A Taron Majalisar Zartarwa Na Makon Nan

by Leadership Hausa
9 months ago
in Siyasa
0
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rantsar da Honarabul Bala Aliyu Gusau a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) a wani ɓangare na shirye-shiryen gwamnatinsa gabanin zaɓen ƙananan hukumomi.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Litinin a yayin taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a zauren majalisar da ke gidan gwamnati a Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa wa’adin manyan shugabannin riƙo na ƙananan hukumin su 14 zai ƙare ne a ranar 23 ga Oktoba, 2024.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, babbar Alƙalin jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, wacce Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u ya wakilta ta rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓen.

zamfara

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

Har ila yau, Gwamna Lawal ya sanar da mambobin majalisar zartarwar jihar yayin zamanta cewa halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 79 da ya yi na da matuƙar amfani.

Ya bayyana fatan hakan zai haifar da sakamako mai kyau a ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar al’ummar Zamfara.

Gwamnan ya ce, ya sanya hannu kan gyaran dokar zaɓe ta jihar Zamfara makwannin da suka gabata gabanin zaɓen ƙananan hukumomin da ke tafe.

Ya ce, “A bisa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a kwanan baya game da zaben ƙananan hukumomi, muna buƙatar mu gudanar da zabe a ƙananan hukumomin mu cikin aminci.

“A bisa ga rattaba hannu kan dokar da aka yi wa kwaskwarima, hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar za ta sanar da jadawalin zaben da wuri-wuri domin mu samu zababbun shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Zamfara.

 

“Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) za ta fito da tsare-tsare kan zaɓen, kuma ana sa ran dukkanmu za mu ba da goyon baya da haɗin kan da ya dace domin samun nasarar aikin.”

Bugu da ƙari, a yayin taron majalisar, Gwamna Lawal ya umurci Sakataren gwamnatin jiha da ya haɗa hannu da mataimakin gwamnan domin gaggauta shirya bikin ƙaddamar da Hukumar Bunƙasa Zuba Jari ta Jihar Zamfara (ZIPA) domin ta yi aiki yadda ya kamata.

zamfarazamfara

Gwamnan ya kuma sanar da majalisar cewa jihar a shirye take ta fara aikin rabon kuɗi na ‘NG-Cares’.

“Aikin zai ttallafa wa marasa galihu, matasa marasa aikin yi da mata a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar. Za a kashe jimillar kuɗi kusan Naira Biliyan 4.9.

“Masu cin gajiyar wannan shiri za su kasance mutane 5000 na matalauta da marasa galihu; ɗaukar matasa da mata marasa aikin yi 6000; tallafin inganta rayuwa rayuwa ga matasa da mata 8000.

“Dole ne mu yi adalci da nuna jagoranci nagari ga dukkan al’ummar jiharmu,” in ji shi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Dauda LawalJihar ZamfaraKananan HukumomiZabeZaɓe
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karo Na 4 Cikin 2024, An Ɗauke Wutar Nijeriya Baki Ɗaya

Next Post

Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba – Tinubu

Related

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

1 day ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

2 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

2 days ago
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna
Siyasa

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

2 days ago
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna
Labarai

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

5 days ago
Next Post
Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu 

Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

July 23, 2025
An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

July 23, 2025
Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

July 23, 2025
Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

July 23, 2025
Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

July 23, 2025
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

July 23, 2025
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

July 23, 2025
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.