• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar

Abubuwan Da Suka Wakana A Taron Majalisar Zartarwa Na Makon Nan

by Leadership Hausa
1 year ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rantsar da Honarabul Bala Aliyu Gusau a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) a wani ɓangare na shirye-shiryen gwamnatinsa gabanin zaɓen ƙananan hukumomi.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Litinin a yayin taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a zauren majalisar da ke gidan gwamnati a Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa wa’adin manyan shugabannin riƙo na ƙananan hukumin su 14 zai ƙare ne a ranar 23 ga Oktoba, 2024.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, babbar Alƙalin jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, wacce Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u ya wakilta ta rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓen.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Har ila yau, Gwamna Lawal ya sanar da mambobin majalisar zartarwar jihar yayin zamanta cewa halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 79 da ya yi na da matuƙar amfani.

Ya bayyana fatan hakan zai haifar da sakamako mai kyau a ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar al’ummar Zamfara.

Gwamnan ya ce, ya sanya hannu kan gyaran dokar zaɓe ta jihar Zamfara makwannin da suka gabata gabanin zaɓen ƙananan hukumomin da ke tafe.

Ya ce, “A bisa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a kwanan baya game da zaben ƙananan hukumomi, muna buƙatar mu gudanar da zabe a ƙananan hukumomin mu cikin aminci.

“A bisa ga rattaba hannu kan dokar da aka yi wa kwaskwarima, hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar za ta sanar da jadawalin zaben da wuri-wuri domin mu samu zababbun shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Zamfara.

 

“Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) za ta fito da tsare-tsare kan zaɓen, kuma ana sa ran dukkanmu za mu ba da goyon baya da haɗin kan da ya dace domin samun nasarar aikin.”

Bugu da ƙari, a yayin taron majalisar, Gwamna Lawal ya umurci Sakataren gwamnatin jiha da ya haɗa hannu da mataimakin gwamnan domin gaggauta shirya bikin ƙaddamar da Hukumar Bunƙasa Zuba Jari ta Jihar Zamfara (ZIPA) domin ta yi aiki yadda ya kamata.

zamfarazamfara

Gwamnan ya kuma sanar da majalisar cewa jihar a shirye take ta fara aikin rabon kuɗi na ‘NG-Cares’.

“Aikin zai ttallafa wa marasa galihu, matasa marasa aikin yi da mata a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar. Za a kashe jimillar kuɗi kusan Naira Biliyan 4.9.

“Masu cin gajiyar wannan shiri za su kasance mutane 5000 na matalauta da marasa galihu; ɗaukar matasa da mata marasa aikin yi 6000; tallafin inganta rayuwa rayuwa ga matasa da mata 8000.

“Dole ne mu yi adalci da nuna jagoranci nagari ga dukkan al’ummar jiharmu,” in ji shi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Next Post
Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu 

Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.