ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada cewa gwamnati da kafafen yaɗa labarai abokan hulɗa ne wajen gina ƙasa, ba ‘yan adawa ba, duk da saɓanin da ake samu a wasu lokuta.

 

Ya bayyana haka ne a yayin ziyarar ban-girma da tawagar gudanarwar kamfanin jaridun The Guardian suka kai ofishin sa ranar Alhamis.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki
  • Mene Ne Ainihin Abun Da Philippines Ta Samu Daga Wajen Amurka?

“Ban yi imani da cewa gwamnati da ‘yan jarida ‘yan adawa ne ba, a’a, abokan hulɗa ne a cikin wannan aiki mai wuyar gaske na gina ƙasa, aikin da ke zuwa da mabanbantan ra’ayoyi da hanyoyi daban-daban,” inji Idris.

 

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Ya bayyana irin rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa a matsayin masu sa ido kan al’umma, inda ya jaddada aikinsu na tabbatar da dimokuraɗiyyar Nijeriya, zaman lafiya, da haɗin kai, waɗanda ke da muhimmanci ga martabar ƙasar a duniya.

 

Ministan ya kuma amince da The Guardian a matsayin babbar kafar yaɗa labarai, wanda tarihi ya danganta da gwagwarmayar dimokraɗiyyar Nijeriya da yaƙi da mulkin soja.

 

Ya buƙaci jaridar da ta ci gaba da jajircewarta kan manufofin dimokuraɗiyya da kuma yin watsi da duk wani tasiri da zai kawo barazana ga zaman lafiyar ƙasa.

 

Idris ya kuma bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta mayar da hankali ne kan kawo sauyi a fannin zamantakewa da tattalin arziƙin Nijeriya.

 

Da yake mayar da martani, Babban Jami’in The Guardian, Toke Ibru, ya tabbatar da aniyar ƙungiyar na inganta haɗin kai, zaman lafiya, da tsaro, tare da bayyana rawar da take takawa a matsayin babbar murya a ci gaban dimokuraɗiyyar Nijeriya.

 

Sauran waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Muƙaddashin Babban Sakatare na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Misis Comfort Ajiboye, tare da wasu manyan jami’an gudanarwar The Guardian, da suka haɗa da Martins Oloja, Dr. Oluwafemi Adekoya, da Chuks. Nwanne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.