• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin nan da aka ƙaƙaba wa masu ajiya a banki na tallafin tsaron yanar gizo.

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya bayyana shigo da harajin kan kuɗaɗen da jama’a da kamfanoni ke turawa, wanda hakan ya haifar da ce-ce-ku-ce.

  • Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
  • Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu – Ƙungiyoyi

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana matakin da gwamnatin ta ɗauka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Fadar Gwamnati da ke Abuja ranar Talata.

Ya ce ana yin nazari kan shirin. “Matsayin gwamnati shi ne an dakatar da wannan shirin. An ɗage shi. Matsayin gwamnati kenan a yanzu. Ana sake sabon nazari a kan sa.
“An maganar sosai a taron Majalisar (FEC) a jiya. Kun san cewa majalisar ta yau (taron) an ɗora ne kan na jiya,” inji ministan.

Ya ƙara da cewa: “Don haka, zan iya gaya maku cewa an dakatar da harajin tsaron yanar gizo. Gwamnati na sake tunani a kan sa.”

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

A ranar 6 ga watan Mayu ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna, masu gudanar da hada-hadar kuɗi ta wayar salula, da masu ba da sabis na biyan kuɗi da su aiwatar da wannan harajin kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar 2024 ta Laifin Yanar Gizo (Hanawa, Rigakafi, da sauran su) (gyara).

An tsara za a riƙa biyan harajin kashi 0.5 cikin ɗari kan duk kuɗin da mutum ya tura wa wani. Za a aika da kuɗaɗen ne zuwa Asusun Ajiyar Tsaron Yanar Gizo na Ƙasa wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA) ke shugabanta.

Sai dai matakin ya fusata mutane matuƙa, lamarin da ya sa ake kira da a dakatar da shi.

A makon da ya gabata ma Majalisar Wakilai ta buƙaci CBN da ya janye umarnin da ya ba bankuna da su fara aiwatar da harajin, inda ta bayyana hakan a matsayin “shubuha”.

Wannan matakin na gwamnati ya kasance a matsayin martani ga wani ƙudiri kan buƙatar gaggawa na dakatarwa da kuma gyara aiwatar da harajin tsaron yanar gizo da ɗan majalisa Kingsley Chinda ya gabatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNGwamnatin TinubuHarajin Tsaron Yanar GizoTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sha’anin Noman Abarba Ke Taimakawa Kyautata Zaman Rayuwar Mazauna Wasu Kauyuka A Kasar Sin

Next Post

Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

12 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Next Post
Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.