• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi da su fara cire harajin tsaro na intanet kan kowani hada-hadar banki da ‘yan Nijeriya za su yi.

A cewar sanarwar da babban bankin ya fitar, za a fara biyan sabon harajin ne nan da mako biyu masu zuwa.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Ga wasu abubuwan da ya dace ku sani kan harajin tsaro na intanet da ‘yan Nijeriya za su dunga biya kamar yadda CBN ya umarta.

Za a rika cire harajin kaso 0.5 cikin dari, kwatankwacin rabin kaso, zai kasance kan dukkanin hada-hadar kudi da aka yi ta yanar gizo ne. Duk kwastoman da ya yi hada-hadar banki ta intanet za a caje shi wannan sabon harajin, kuma bankin da yake ne za su cire kason kai tsaye. Za a sanar da kwastoma ta cikin jadawalin asusun ajiyarsa na cewa an cire wannan kudin.

Haka kuma, bayan bankuna sun cire wannan kudin harajin za su shigar da kudin kai tsaye zuwa asusun harajin tsaron intanet na kasa da ke ofishin babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro. Za a fara aiwatar da cire kudin ne nan da mako biyu daga ranar da CBN ta sake sanarwa, ranar 6 ga watan Mayu, kuma bankuna za su shigar da kudin zuwa asusun NCF ne a dunkule.

Labarai Masu Nasaba

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Sannan bankuna za su amfani da tsarin da ke cire harajin da shigar da shi asusun da aka ware. Dukkanin bankin da ya kasa shigar da wannan harajin akwai cin tara da za a yi masa da suka hada da cire kaso biyu cikin dari na kason wannan bankin na shekara-shekara.

Sai dai kum, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da wannan umurnin na babban banki kan cire kasha 05 na harajin tsaro ga kowani hada-hadar kudi ta intanet.

Shugaban NLC, Joe Ajaero shi ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Abuja.

Ajaero ya dai yi watsi da sanarwar CBN kan wannan haraji da zai fara aiki nan da wakonni biyu.

A cewar Ajaero, NLC ta yi Allah wadai da wannan mataki tare da kiran gwamnatin tarayya ta gaggauta janye matakin.

Ya ce kakaba wannan harajin zai tagayyara ‘yan kara fiye da halin da ake ciki a yanzu.

Ita kungiyar kokarin tabbatar da adalci ta SERAP ta nuna adawarta da sabon harajin na tsaron intanet.

Kungiyar ta bukaci Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu da ya bai wa Babban Bankin Nijeriya umarnin soke harajin kafin nan da awa 48 kasancewar ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma walwalar al’umma.

Wannan haraji zai zamo doriya ne a kan jerin haraje-haraje da al’ummar Nijeriya ke biya wadanda babban bankin kasar ya kakaba musu.

Cikin su akwai harajin kula da katin ATM, da kula da asusun ajiya, harajin gwamnati, cajin tura kudi daga wani banki zuwa wani da kuma harajin tura kudi ta laturoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BakunaCBNHarajiIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

Related

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

3 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

7 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

9 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

9 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

10 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.