ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin nan da aka ƙaƙaba wa masu ajiya a banki na tallafin tsaron yanar gizo.

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya bayyana shigo da harajin kan kuɗaɗen da jama’a da kamfanoni ke turawa, wanda hakan ya haifar da ce-ce-ku-ce.

  • Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
  • Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu – Ƙungiyoyi

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana matakin da gwamnatin ta ɗauka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Fadar Gwamnati da ke Abuja ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya ce ana yin nazari kan shirin. “Matsayin gwamnati shi ne an dakatar da wannan shirin. An ɗage shi. Matsayin gwamnati kenan a yanzu. Ana sake sabon nazari a kan sa.
“An maganar sosai a taron Majalisar (FEC) a jiya. Kun san cewa majalisar ta yau (taron) an ɗora ne kan na jiya,” inji ministan.

Ya ƙara da cewa: “Don haka, zan iya gaya maku cewa an dakatar da harajin tsaron yanar gizo. Gwamnati na sake tunani a kan sa.”

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

A ranar 6 ga watan Mayu ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna, masu gudanar da hada-hadar kuɗi ta wayar salula, da masu ba da sabis na biyan kuɗi da su aiwatar da wannan harajin kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar 2024 ta Laifin Yanar Gizo (Hanawa, Rigakafi, da sauran su) (gyara).

An tsara za a riƙa biyan harajin kashi 0.5 cikin ɗari kan duk kuɗin da mutum ya tura wa wani. Za a aika da kuɗaɗen ne zuwa Asusun Ajiyar Tsaron Yanar Gizo na Ƙasa wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA) ke shugabanta.

Sai dai matakin ya fusata mutane matuƙa, lamarin da ya sa ake kira da a dakatar da shi.

A makon da ya gabata ma Majalisar Wakilai ta buƙaci CBN da ya janye umarnin da ya ba bankuna da su fara aiwatar da harajin, inda ta bayyana hakan a matsayin “shubuha”.

Wannan matakin na gwamnati ya kasance a matsayin martani ga wani ƙudiri kan buƙatar gaggawa na dakatarwa da kuma gyara aiwatar da harajin tsaron yanar gizo da ɗan majalisa Kingsley Chinda ya gabatar.

Gwamnati
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Next Post
Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.