• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Gwamnati Ta Nemi Zuba Jari A Fasahar Na’urar Hoto Da Ke Tashoshin Jiragen Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bukaci kamfanoni masu zaman kansu da su zuba jari a bangaren fasahar na’urar daukar hoto ta (Scanning) a tashoshin jiragen ruwan Nijeriya domin dorewar amfani da ita da kuma bunkasa amfani da zamani a harkokin safarar jiragen ruwa a kasar nan.

Wannan bukatar ta fito ne a wajen ganawar bullo da dabarun hanyoyin da za a inganta jiragen ruwa da samar da tsarin kara samar da kudaden shiga da aka  yi a gudana a Abuja, wanda ya samu halartar ministan kula da teku da albarkatun cikin teko Gboyega Oyetola; ministan sufuri, Said Ahmed Alkali; kwanturola-janar na hukumar hana fasa kwabri wato Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da kuma darakta janar na hukumar kula da layukan dogo na Nijeriya (NRC), Fidet Okhiria.

  • Kasashen Afirka 10 Da Za Su Samu Bunkasar Tattalin Arziki A 2024
  • Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

A wani mataki na inganta ayyukan jiragen ruwa a tashoshin jiragen ruwa da kuma ganin sun yi gogayya da takwarorinsu, ministoci da shugaban kwastam din sun amince kan cewar dole ne a samar da matakin duba jiragen ruwa na zahiri a filayen jiragen ruwa da samar da hadin guiwa da saukaka aiki domin kyautata kasuwanci.

Kudurin na kunshe ta cikin sanar hadin guiwa da kakakin ministan da kula da albarkatun tekuna, Ismail Omipidan da na kwastam spokesman, Abdullahi Maiwada.

Ministocin sun bayyana muhimmancin amfanin na’urar kimiyya ta dubawa da tantancewa wato (NIIT) wajen rage cinkoso a filayen jirage, kuma bai wa shugaban kwastam ikon tantancewa kayan da jirgin ruwa ya dauko cikin sauki da hanzari ta hanyar daukan hoton scanning cikin ‘yan mintuna sabanin hanyar da ake amfani da shi na dube-duben zahiri wanda hakan ne dauka tsowon lokaci kuma wasu lokutan ba a samun biyan bukata yadda ake so.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Don haka ne suka ce, amfani da fasahar daukan hoton zai kawo sauki sosai kuma zai taimaka wajen kyautata tsaro da rage matsatsin aiki hadi da taimaka wa kasar na sosai.

Don haka ne suka nemi masu hannu da shuni da su zuba hannun jarinsu wajen kawo na’urar daukan hotuna a filayen jiragen ruwa domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Sun kuma cimma matsayar cewa za a sake gina sabuwar layin dogo a gefen na’urar daukan hoto da ke filin jirgin ruwan Apapa domin tabbatar da rage cinkso da bada damar saukaka aikin daukan hoton cikin sauki da hanzari.

 Sun kuma cimma matsayar sake kwaskwarima da tabbatar da ana amfani da naurorin daukan hotuna da ake da su a halin yanzu a wasu jiragen jiragen ruwa kamar su na Apapa, Tincan Island, Onne, da PTML domin tabbatar da amfaninsu da cin gajiyarsu, kuma na’urar salula na daukan hotona su ma za a tabbatar da zuba su a muhumman filayen jiragen ruwa domin saukaka aikin duba jiragen ruwa da kayan da suka kwaso.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

Next Post

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da É—umi-É—uminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

5 days ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

6 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

11 months ago
Next Post
Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

Dabarun Kiwon Zomo A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun KaÉ—u MatuÆ™a Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.