Gwamnatin jihar Bauchi ta baje kolin sabon tsarin neman ƙirƙirar sabbin masarautu, Sarakuna, da gundumomi. Wannan mataki ya biyo bayan alƙawarin da Gwamna Bala Muhammad ya yi a lokacin zaɓensa.
Kwamishinan hulɗa da Jama’a, Mukhtar Gidado, ya bayyana cewa za a buɗe taron karɓar buƙatu daga ranar 10 ga Yuni zuwa 8 ga Yuli 2025. Dukkan buƙatun za a aika zuwa ofishin Babban Sakataren Ma’aikatar ƙananan hukumomi.
- An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa
- An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Ana buƙatar masu nema su gabatar da takardun da suka ƙunshi:
– Cikakken bayanin sabuwar masarauta ko gunduma
– Taswirar yankin da ke neman rabuwa
– Bayanan al’umma da tarihin yankin
– Sahihancin hannun sarakuna da shugabannin al’umma
Gwamnatin ta jaddada cewa wannan shiri na daga cikin ƙoƙarin bunƙasa al’adu da ƙarfafa zaman lafiya ta hanyar inganta tsarin mulkin gargajiya.
Dukkan al’ummomin da ke da ra’ayin ƙirƙirar sabon masarauta ko gunduma ana ƙarfafa su su gabatar da buƙatunsu a cikin waɗannan kayan da aka kayyade.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp