A wani mataki na yunkurin cika alkawuran da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya dauka a lokacin yakin neman zaben da ya gabata da kuma kiranye-kiranyen da aka samu daga sassan jihar, gwamantin jihar ta yi kira ga al’ummomin da suke da ra’ayi kuma suke so, da su mika bukatar neman kirkirar sabbin masarautun gargajiya, sarakuna ko gundumomi.
Mashawarcin gwamnan Jihar Bauchi kan hulda da ‘yan jarida, Kwamared Mukhtar Gidado shi ne ya sanar da wannan matakin ta cikin sanarwar da ya fitar a ranar Litinin, inda ya ce, za a bude damar amsar bukatar ne daga ranar Talata 10 ga watan Yuni zuwa 8 ga watan Yulin 2025.
- Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
- Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
Dukkanin bukatar nema za a aike ne zuwa ofishin babban sakataren ma’aikatar kananan hukumomi da kula da harkokin masarautun gargajiya da ke cikin Abubakar Umar Secretariat ta Bauchi.
Gidado ya kara da cewa kowani bukatar nuna sha’awar nema dole ne a fitar da shi har kwafi guda 15.
Gwamnatin jihar ya kuma ce dole ne kowani bukata ya zama an samar da muhimmin shafin farko da zai kunshi cikakken sunan masarauta, sarki ko gundumar da ake nema, tare kuma da bayyana balo-balo kan sunan masarauta ko gundumar da karamar hukumar da ake neman sabon masarautar ko sarki ya fito daga ciki.
A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.
Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.
Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.
Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.
Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.
Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp