• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Shari’a Abubakar Malami (SAN), ya bayyana cewa gwamnatin Buhari za ta yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da tsaron kasar nan kafin karewar wa’adinsa.

Malami ya bayyana hakan ne a cikin sakon murnar sallar ga al’ummar Musulmin kasa da na Jihar Kebbi kan murnar zagayowar sallah.

  • Jaridar Daily Trust Ba Ta Yi Mana Adalci Ba- Fadar Shugaban Kasa 
  • Mataimaki: Gwamnonin APC Na Alfahari Da Zabin Tinubu – Bagudu

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takarar da sakataren yada labaransa, Ibrahim Abubakar Dakingari, na kungiyar Khadimmiya da ya sanyawa hannu aka kuma rabawa manema labarai a Brinin Kebbi.

Minista ya ce”Bikin sallah na tunatar da musulmi da su kasance masu biyayya da zuciya daya ga umarni da dokokin Allah madaukakin Sarki kamar yadda Annabi Ibrahim, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi.”

“Gudanar da wannan gagarumin biki, ya kamata mu yi tunani a kan darussa na asali na hakuri, sadaukarwa da mika wuya ga yardar Allah da Annabi Ibrahim ya nuna a lokacin da Allah ya umarce shi da ya yanka dansa tilo (Isma’ila), ta hanyar sadaukar da kanmu ga kara riko da dokokin Ubangiji da kuma nuna hakikanin ruhin Musulunci a cikin dukkan ayyukanmu.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Yayin da mu ke bikin babbar sallah, dole ne mu yi la’akari da duk abubuwan da ke faruwa a kasarmu, domin mu yi amfani da lokacin yin addu’a don Allah ya kawo mana dauki ga matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke addabar kasar nan wanda gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke ciki, inji shi”.

Haka kuma ministan ya kuma yi kira ga ’yan uwanmu maza da mata a kasa mai tsarki da suke gudanar da aikin hajjin bana da su yi ta addu’a domin neman fansa.

“Ina kara sake tabbatar muku cewa gwamnatin Buhari za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da tsaron kasar nan.

“Ina addu’ar Allah ya karbi addu’o’inmu na ganin an samu dawamammen zaman lafiya a jihar Kebbi da kasa baki daya tare da samar da zaman lafiya a siyasance,” in ji Malami.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKebbiMalamiMatsalar TsaroWa'adin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jaridar Daily Trust Ba Ta Yi Mana Adalci Ba- Fadar Shugaban Kasa 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

3 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

7 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

10 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

12 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

13 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba - Matawalle

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.