• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin Gombe

Tawagar gwamnatin jihar Gombe karkashin jagorancin kwamishinan da ke sanya ido a ma’aikatar muhalli da gandun daji, Shehu Ibrahim Madugu, ta ziyarci wasu al’ummomin da ambaliyar ruwa ta shafa a garin Bajoga da ke karamar hukumar Funakaye.

Ziyarar ta’aziyya da tantance barnar da tawagar gwamnatin jihar ta kai ya biyo bayan umarnin da gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar ga ma’aikatar muhallin da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da hukumomin da abin ya shafa kan gaggauta ziyar tare da tantance irin barnar da ambaliyar ta yi, tare da bada tallafi ga wadanda ibtila’in ya shafa don saukaka musu radadi.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi

Sauran ‘yan tawagar gwamnatin jihar sun hada da kwamishinan tsaron cikin gida da kyautata tarbiyya, Adamu Dishi Kupto, da babban sakataren ma’aikatar muhalli, Ibrahim Sule Bage da wakilin hukumar bada agajin gaggawa (SEMA) da sauransu.

Tawagar ta samu tarba daga shugaban karamar hukumar Funakaye, Alhaji Ibrahim Cheldu da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka zagaya da su yankunan da lamarin ya shafa.

A jawabinsa yayin ziyarar, kwamishina Shehu Ibrahim Madugu, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa na gwamna Inuwa Yahaya, bisa asarar rayuka da dukiyoyi da ambaliyar ta shafa a karamar hukumar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

“Makasudin zuwanmu a yau shi ne mu jajanta tare da mika ta’aziyyarmu gare ku bisa wannan ibtila’in daya shafe ku, tare da tantance barnar da ambaliyar ta haifar da nufin bai wa gwamnati shawara don samar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa”.

Sai ya bukaci al’ummomin da ke fuskantar matsalar ambaliya su yi biyayya ga hasashen ambaliyar ruwa da gargadin da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NIMET) ta yi.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Funakaye, Ibrahim Adamu Cheldu, ya yaba wa gwamna Inuwa Yahaya, bisa umarnin gaggawa da ya bayar wajen taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da bada tabbacin majalisarsa cewa a shirye take ta mara wa gwamnatin jihar baya a kowane lokaci.

Tawagar ta kuma ziyarci Mai Martaba Sarkin Funakaye, Alhaji Muazu Mohammed Kwairanga tare da jajanta masa bisa ibtila’in daya samu al’ummar tasa.

Idan za a iya tunawa wani yaro dan shekaru uku ya rasu yayin da dan uwansa dan shekaru biyu ya samu munanan raunuka sakamakon mamakon ruwan sama da ya yi barna a wasu yankunan garin Bajoga da suka hada da Shara-Mansur da Bodoriyel.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Shara Mansur, da Jillahi da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.