• Leadership Hausa
Tuesday, March 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye

by Khalid Idris Doya
8 months ago
in Kananan Labarai
0
Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar gwamnatin jihar Gombe karkashin jagorancin kwamishinan da ke sanya ido a ma’aikatar muhalli da gandun daji, Shehu Ibrahim Madugu, ta ziyarci wasu al’ummomin da ambaliyar ruwa ta shafa a garin Bajoga da ke karamar hukumar Funakaye.

Ziyarar ta’aziyya da tantance barnar da tawagar gwamnatin jihar ta kai ya biyo bayan umarnin da gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar ga ma’aikatar muhallin da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da hukumomin da abin ya shafa kan gaggauta ziyar tare da tantance irin barnar da ambaliyar ta yi, tare da bada tallafi ga wadanda ibtila’in ya shafa don saukaka musu radadi.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi

Sauran ‘yan tawagar gwamnatin jihar sun hada da kwamishinan tsaron cikin gida da kyautata tarbiyya, Adamu Dishi Kupto, da babban sakataren ma’aikatar muhalli, Ibrahim Sule Bage da wakilin hukumar bada agajin gaggawa (SEMA) da sauransu.

Tawagar ta samu tarba daga shugaban karamar hukumar Funakaye, Alhaji Ibrahim Cheldu da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka zagaya da su yankunan da lamarin ya shafa.

A jawabinsa yayin ziyarar, kwamishina Shehu Ibrahim Madugu, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa na gwamna Inuwa Yahaya, bisa asarar rayuka da dukiyoyi da ambaliyar ta shafa a karamar hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Gwamnoni: Ku Ankare Akwai Masu Shaidar Aikin Tsaro Ta Bogi, INEC Ga Masu Zabe

Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4

“Makasudin zuwanmu a yau shi ne mu jajanta tare da mika ta’aziyyarmu gare ku bisa wannan ibtila’in daya shafe ku, tare da tantance barnar da ambaliyar ta haifar da nufin bai wa gwamnati shawara don samar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa”.

Sai ya bukaci al’ummomin da ke fuskantar matsalar ambaliya su yi biyayya ga hasashen ambaliyar ruwa da gargadin da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NIMET) ta yi.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Funakaye, Ibrahim Adamu Cheldu, ya yaba wa gwamna Inuwa Yahaya, bisa umarnin gaggawa da ya bayar wajen taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da bada tabbacin majalisarsa cewa a shirye take ta mara wa gwamnatin jihar baya a kowane lokaci.

Tawagar ta kuma ziyarci Mai Martaba Sarkin Funakaye, Alhaji Muazu Mohammed Kwairanga tare da jajanta masa bisa ibtila’in daya samu al’ummar tasa.

Idan za a iya tunawa wani yaro dan shekaru uku ya rasu yayin da dan uwansa dan shekaru biyu ya samu munanan raunuka sakamakon mamakon ruwan sama da ya yi barna a wasu yankunan garin Bajoga da suka hada da Shara-Mansur da Bodoriyel.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Shara Mansur, da Jillahi da dai sauransu.

Tags: Ambaliyar RuwaGwamna Inuwa MohammedGwamnatin GombeMamakon Ruwan SamaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Gudanar Da Taron Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Na Duniya Na Shekarar 2022 A Shanghai

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

Related

INEC Ta Kara Wa’adin Karbar Katin Zabe
Kananan Labarai

Zaben Gwamnoni: Ku Ankare Akwai Masu Shaidar Aikin Tsaro Ta Bogi, INEC Ga Masu Zabe

3 days ago
Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4
Kananan Labarai

Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4

1 month ago
Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil
Kananan Labarai

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

2 months ago
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara
Kananan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

2 months ago
Tambuwal Ya Gabatar Da Kasafin Kudinsa Na Karshe a Sakkwato
Kananan Labarai

Tambuwal Ya Gabatar Da Kasafin Kudinsa Na Karshe a Sakkwato

3 months ago
Tambari ‘TV’ Ta Nada Shawai A Matsayin Daraktan Gudanarwarta
Kananan Labarai

Tambari ‘TV’ Ta Nada Shawai A Matsayin Daraktan Gudanarwarta

4 months ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Rahoto Game Da Halin Dimokuradiyya A Amurka A Shekarar 2022

Sin Ta Fitar Da Rahoto Game Da Halin Dimokuradiyya A Amurka A Shekarar 2022

March 21, 2023
Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

March 21, 2023
An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

March 20, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

March 20, 2023
Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

March 20, 2023
Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

March 20, 2023
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

March 20, 2023
Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

March 20, 2023
Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

March 20, 2023
An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

March 20, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.