ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gwamnatin Gombe

Tawagar gwamnatin jihar Gombe karkashin jagorancin kwamishinan da ke sanya ido a ma’aikatar muhalli da gandun daji, Shehu Ibrahim Madugu, ta ziyarci wasu al’ummomin da ambaliyar ruwa ta shafa a garin Bajoga da ke karamar hukumar Funakaye.

Ziyarar ta’aziyya da tantance barnar da tawagar gwamnatin jihar ta kai ya biyo bayan umarnin da gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar ga ma’aikatar muhallin da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da hukumomin da abin ya shafa kan gaggauta ziyar tare da tantance irin barnar da ambaliyar ta yi, tare da bada tallafi ga wadanda ibtila’in ya shafa don saukaka musu radadi.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi

Sauran ‘yan tawagar gwamnatin jihar sun hada da kwamishinan tsaron cikin gida da kyautata tarbiyya, Adamu Dishi Kupto, da babban sakataren ma’aikatar muhalli, Ibrahim Sule Bage da wakilin hukumar bada agajin gaggawa (SEMA) da sauransu.

ADVERTISEMENT

Tawagar ta samu tarba daga shugaban karamar hukumar Funakaye, Alhaji Ibrahim Cheldu da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka zagaya da su yankunan da lamarin ya shafa.

A jawabinsa yayin ziyarar, kwamishina Shehu Ibrahim Madugu, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa na gwamna Inuwa Yahaya, bisa asarar rayuka da dukiyoyi da ambaliyar ta shafa a karamar hukumar.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“Makasudin zuwanmu a yau shi ne mu jajanta tare da mika ta’aziyyarmu gare ku bisa wannan ibtila’in daya shafe ku, tare da tantance barnar da ambaliyar ta haifar da nufin bai wa gwamnati shawara don samar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa”.

Sai ya bukaci al’ummomin da ke fuskantar matsalar ambaliya su yi biyayya ga hasashen ambaliyar ruwa da gargadin da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NIMET) ta yi.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Funakaye, Ibrahim Adamu Cheldu, ya yaba wa gwamna Inuwa Yahaya, bisa umarnin gaggawa da ya bayar wajen taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da bada tabbacin majalisarsa cewa a shirye take ta mara wa gwamnatin jihar baya a kowane lokaci.

Tawagar ta kuma ziyarci Mai Martaba Sarkin Funakaye, Alhaji Muazu Mohammed Kwairanga tare da jajanta masa bisa ibtila’in daya samu al’ummar tasa.

Idan za a iya tunawa wani yaro dan shekaru uku ya rasu yayin da dan uwansa dan shekaru biyu ya samu munanan raunuka sakamakon mamakon ruwan sama da ya yi barna a wasu yankunan garin Bajoga da suka hada da Shara-Mansur da Bodoriyel.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Shara Mansur, da Jillahi da dai sauransu.

Gwamnatin Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.