• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Jihar Enugu Ta Haramta Hakar Ma’adinai Ta Haramtacciyar Hanya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Enugu ta sanar da hana hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba a fadin jihar.

Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Chidiebere Onyia, ne ya sanar da dakatarwar a ranar Juma’a a Enugu, yayin da yake kaddamar da kwamitin da zai duba ayyukan hakar ma’adanai a jihar.

  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Enugu
  • ‘Yan Awaren Biyafara 30 Sun Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Enugu

Onyia ya yi gargadi tare hukunta duk wani mai hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ko wanda ya saba wa umarnin gwamnati.

Ya ce, “Gwamnati ta lura cewa yana da matukar amfani ga jama’a su kare kansu daga duk wani hadari ko gurbacewar yanayi, tare da tabbatar da daidaiton hakkokin fa’idojin da za a iya samu daga duk wani albarkatun ma’adinai ga mutanen Enugu.”

A cewarsa, haramcin ya biyo bayan umarnin Gwamna Peter Mbah kan rahoton gano albarkatun ma’adinai a wasu yankuna da kuma hakar albarkatun ba tare da izinin gwamnati ba.

Labarai Masu Nasaba

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

An ruwaito cewa kwamitin na karkashin jagorancin kwamishinan muhalli, Farfesa Sam Ugwu.

Mambobin sun hada da babban lauya kuma kwamishinan shari’a, Dr Kingsley Udeh, mai bawa gwamna shawara na musamman kan makamashi da albarkatu, Kingsley Nnaji, mai bawa gwamna shawara na musamman akan harkokin shari’a, Osinachi Nnajieze, da babban jami’in tsaro na gidan gwamnati, Mr Alex. Akinlalu.

Sauran mambobin sun hada da babban mataimaki na musamman ga gwamna kan harkokin tsaro, Onyeator Vincent, babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan harkokin yada labarai, Dan Nwomeh, babban mataimaki na musamman ga gwamna kan hulda da kasashen waje, Uche Chukwu, da kuma mai taimakawa gwamna na musamman kan kudaden shiga, Sandra George.

Sakataren gwamnatin ya ce ayyukan kwamitin sun hada da gano wuraren hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, dakatar da duk wani aikin hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, duba duk wasu takardun tantance muhalli na duk kamfanonin hakar ma’adanai da kuma sake tantancewa da sake tabbatar da duk kamfanonin hakar ma’adanai a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EnuguHakar Ma'adinaiHaramta Hakar Ma'adinaiInugu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mitocin Lantarki Miliyan 5.3 Na Fuskantar Barazanar Daina Aiki

Next Post

Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

Related

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

45 minutes ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

2 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

14 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

16 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

22 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

23 hours ago
Next Post
Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.