ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowa Hutu: Iyaye Sun Koka Kan Karin Kudin Makaranta A Yanayin Kuncin Rayuwa

by CMG Hausa
3 years ago
Kudin makaranta

A daidai lokacin da makarantun firamare da sakandire da ke fadin kasar nan suka shiga sabon zangon karatu bayan dawowa daga hutu, galibin iyaye sun koka da karin kudin makaranta a yanayin kuncin rayuwa da ake ciki a halin yanzu, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya nuna.

Wannan karin kudin ya zo daidai lokacin da ake samun raguwar kudaden shiga da zai dauki nauyin iyalai, saboda hauhawar farashin kayayyaki a fadin kasar nan sakamakon cire tallafin man fetur.

  • Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

Iyayen daliban makarantun gaba da sakandare sun bayyana damuwarsu game da karin kudin makaranta a wasu jami’o’in Nijeriya. Wadannan jami’o’in, sun danganta karin kudaden na kashi 100 zuwa 200 bisa rashin isasshen tallafin kudi daga gwamnati da kuma hauhawar farashin kayayyaki.

ADVERTISEMENT

Duk da kokarin da gwamnati ke yi na aiwatar da tallafin karatu ga daliban da ba su da galihu, mafi yawancin daliban ba su da tabbas game da makomarsu karatunsu.

Har ila yau, tashin hankali na kara karuwa a wasu jami’o’i, yayin da dalibai ke bayyana rashin jin dadinsu kan karin kudin makaranta da aka yi a baya-bayan nan, wanda ya haifar da zanga-zanga a fadin kasar nan. Misali, a kwanakin baya ne daliban Jami’ar Jos suka fito kan tituna domin nuna rashin amincewarsu da karin kudin makaranta da jami’a ta yi.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Masu zanga-zangan karkashin jagorancin kungiyar dalibai ta kasa, sun bukaci a gaggauta dawo da kudin makarantar yadda yake a baya. Masu zanga-zangan dauke da alluna masu dauke da sako kamar haka, “Idan yaranku za su iya biyan kudin, mu ba za mu iya ba” da “Ba ma son barin makaranta,” daliban sun bayyana kokensu.

Sun jaddada cewa tuni ‘yan Nijeriya suka fara kokawa da matsalolin tattalin arziki, kuma karin kudin makarantar zai kara ta’azzara lamarin. Zanga-zangar lumana da daliban suka gudanar ta haifar da cunkoson ababen hawa tare da toshe hanyoyin shiga harabar jami’ar.

Haka kuma, a jami’ar Legas (UNILAG), an samu ta tashin hankali a harabar jami’ar, yayin da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) ta goyi bayan daliban na shirya zanga-zanga. Hasali ma, kwanan nan NANS ta ba da wa’adin sa’o’i 48 ga hukumomin jami’ar Legas da su sauya karin kudin makaranta.
NANS ta kuma yi kira ga daukacin manyan makarantu da ke fadin kasar nan su guji kara kudin makaranta, sannan ta yi gargadin cewa a shirye suke su hada kan mambobinsu a fadin kasar domin gudanar da zanga-zanga na rashin amincewarsu da irin wadannan karin kudin makaranta.

Ta bayyana wannan matsayar ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa da ke Legas, biyo bayan dakile zanga-zangar lumana da ‘yansanda suka yi a UNILAG.

Kafin haka dai, NANS ta nuna rashin amincewarta da karin sama da kashi 300 na kudaden makaranta a jami’ar Ambrose Alli ta jihar Edo da ke Ekpoma. Daliban hadu a harabar kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) na Jihar Edo, daliban sun bukaci a sake duba kudaden makarantar cikin gaggawa domin a samu zaman lafiya.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa tsadar rayuwa da tsadar kayayyakin aiki na kawo cikas ga ilimi, wanda hakan ya sa iyaye da dama ba su iya saka ‘ya’yansu a makaranta.
Makarantu masu zaman kansu sun kara wa daliban firamare da sakandire kudin makaranta sama da kashi 300, lamarin da ya kara haifar da fargabar cewa yawan daliban ba za su koma makaranta ba. Wasu iyaye na tunanin sanya ‘ya’yansu a makarantun gwamnati, yayin da wasu kuma ba su da tabbas kan matakin da za su dauka nan gaba, wanda haka zai kara haifar da karuwar yaran da ba sa zuwa makaranta.

Makarantu masu zaman kansu sun kara da cewa suna fuskantar tsadar kayayyakin koyo da kamarantarwa, wanda hakan ta sa dole ne su kara kudin makaranta.
Yayin da wasu malaman makarantu masu zaman kansu sun bayyana cewa suna fuskantar karancin albashi.

Kudin makaranta
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.