• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

by Sulaiman and Abubakar Abba
3 weeks ago
Dabbobi

Gwamnatin Jihar Taraba, ta bayyana kudurinta na yi wa kasuwannin sayar da dabbobi guda tara na jihar garanbawul tare da kuma gyara mayankar dabbobi biyar da ke jihar.

 

Hakan na daga cikin kokarin da gwamnatin ke yi na samar da dabaru, domin cin gajiyar da ke fannin.

  • An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
  • Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Kwamishinan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci na jihar, Farfesa Nicholas Oliber Namessan, ya sanar da hakan ne inda ya ce; aikin zai taimaka wajen inganta tsafta da kuma kula da lafiyar dabbobin.

 

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Ya kara da cewa, Allah ya albarkaci Jihar Taraba da dimbin dabbobi, wanda kuma gwamnatin jihar za ta yi dukkan mai yiwuwa, wajen samar da kayan aiki tare da kara bunkasa fannin kiwo na jihar.

 

Kazalika, ya sanar da cewa; gwamnatin za kuma ta tabbatar da ta kara bunkasa kasuwancin fannin, musamman domin wadanda suke a fannin su kara samun kudaden shiga tare da kuma kara samar wa da gwamnatin kudaden shiga.

 

Nicholas, ya sanar da hakan ne, ta bakin wakilinsa Daraktan Kula da Harkokin Dabbobi da ke Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci na jihar, Daudu A. Mbaamo

 

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, har yanzu fannin aikin noma, da shi jihar ta dogara a kai, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gudumawa wajen kara samar da wadataccen abinci a jihar da kuma kara samar da ayyukan yi.

 

Haka zalika, ya koka da cewa; duk a irin wadannan dimbin albarkatun noma da kuma yawan dabbobin da Allah ya wadaci jihar da su, amma har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar kalubalen karancin kasuwannin sayar da dabbobin.

 

Kwamishinan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta himmatu, wajen kara habaka fannin kiwon jihar, wanda tuni ta tuntubi ‘yan kwangilar da za su yi aikin gyaran mayankar tare kuma da samar da kayan aiki na bunkasa kiwon dabbobi a jihar.

 

“Fannin kiwon dabbobi, na daya daga cikin fannonin da ke habaka tattalin arzikin Jihar Taraba da samar da wadataccen abinci da samar da ayyukan yi da kuma kara samar da kudaden shiga, “ a cewar Kwamishinan.

 

“Hakan ne ya sanya gwamnatin jihar, za ta samar da kayan aiki a fannin kiwon jihar, musamman domin cin gajiyar da ake da ita, daga fannin wanda kuma hakan zai amfanar da al’ummar jihar, in ji Nicholas.

 

A jawabinsa tun da farko, jami’in aikin tallafa wa kiwon dabbobi na L-PRES Hananiah Albert, ya jaddda kudurin aikin wajen ganin an cimma burin da aka sanya a gaba.

 

“Za mu tabbatar da mun bi dukkannin ka’idojin da suka dace, wajen wanzar da wannan aiki, domin cimma nasarar da aka sanya a gaba, “in ji Albert.

 

Ya kara da cewa, manufar aikin ita ce; domin mayar da hankali wajen habaka fannin hada-hadar kasuwancin kiwon na dabbobi da kuma kara bunkasa tattalin arzikin fannin tare da tabbatar da kula da lafiyar dabbobi a fadin jihar.

 

A cewarsa, a yanzu haka; akwai sama da kasuwannin sayar da dabbobi goma da ake gudanar da hada-hadar a kowane mako, wanda kuma suke da bukatar a yi musu garanbawu domin samar da saukin gudanar da yin hada-hada a cikinsu tare da kuma samar da tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.