• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa Sojojin Da Suka Kashe ‘Yan Bindiga 152 Tare Da Lalata Sansani 100

by Sadiq
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa Sojojin Da Suka Kashe ‘Yan Bindiga 152 Tare Da Lalata Sansani 100

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 152 tare da lalata sansaninsu sama da 100 a karo na biyu da na uku a 2022.

Mista Samuel Aruwan, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin da yake gabatar da rahoton yanayin tsaro na kashi na biyu da na uku na shekarar 2022, ga gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai.

  • ‘Gaskiyar Lamari Game Da Zargin Amfani Da Sinadarin Mercury A Rigakafin Yara’
  • Xi Ya Yi Jawabi Ga Taron COP14 Kan Kiyaye Filaye Masu Dausayi

Aruwan ya ce dakarun kasa da ke kewayen jihar sun kashe ‘yan bindiga 152.

A cewarsa, an kashe ‘yan bindiga da dama a lokacin da aka kai farmaki ta sama kan sansanonin da aka gano, inda ya ce an kashe ‘yan bindiga 16 a wani rikici a kananan hukumomin Birnin Gwari da Chikun, sannan an lalata sansanoni sama da 100 da ‘yan ta’adda suka mamaye.

Sai dai Aruwan ya ci gaba da cewa a cikin wannan lokaci jami’an tsaro sun ceto mutane 74 da aka yi garkuwa da su.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

Ya kuma bayyana cewa, makaman da aka kama daga hannun ‘yan bindigar a cikin watanni shidan sun hada da, manyan bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK-47 guda saba’in da hudu, AK-49 guda daya da kuma bindigogi kirar 06 guda tara.

Sauran sun hada da bindigogi masu wuta guda hudu, bindigogin fanfo guda hudu, bindiga g3 daya, bindigu na gida guda goma sha shida da kuma harsashi guda 5,398.

Ya kuma bayyana cewa an kwato haramtattun abubuwa daga hannun wadanda ake zargin.

Ya ce adadin haramtattun abubuwan da aka kama sun kai kilogiram 2,759.891 na tabar wiwi da miyagun kwayoyi.

Ya kara da cewa an samu ci gaba sosai a hanyar Kaduna zuwa Abuja, inda ya ce kashe-kashe da garkuwa da mutane a hanyar Kaduna zuwa Abuja ya ragu matuka a kashi na uku, ya kara da cewa kokarin hadin gwiwar yana samun sakamako mai kyau.

Aruwan, wanda ya bayyana godiyarsa ga kwamandoji, hafsoshi da jami’an tsaro da suke aiki dare da rana don ganin an kyautata wa kowa, ya kuma bukaci jami’an tsaro da kada su yi kasa a gwiwa, wajen dakile hare-hare.

Tags: AbujaDakaruDakile HariHariKadunaKisaSojojiYan bindiga
Previous Post

‘Gaskiyar Lamari Game Da Zargin Amfani Da Sinadarin Mercury A Rigakafin Yara’

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Related

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

1 day ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

1 day ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

1 day ago
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike
Manyan Labarai

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

2 days ago
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari
Manyan Labarai

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

2 days ago
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.