ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa Sojojin Da Suka Kashe ‘Yan Bindiga 152 Tare Da Lalata Sansani 100

by Sadiq
4 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 152 tare da lalata sansaninsu sama da 100 a karo na biyu da na uku a 2022.

Mista Samuel Aruwan, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin da yake gabatar da rahoton yanayin tsaro na kashi na biyu da na uku na shekarar 2022, ga gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai.

  • ‘Gaskiyar Lamari Game Da Zargin Amfani Da Sinadarin Mercury A Rigakafin Yara’
  • Xi Ya Yi Jawabi Ga Taron COP14 Kan Kiyaye Filaye Masu Dausayi

Aruwan ya ce dakarun kasa da ke kewayen jihar sun kashe ‘yan bindiga 152.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, an kashe ‘yan bindiga da dama a lokacin da aka kai farmaki ta sama kan sansanonin da aka gano, inda ya ce an kashe ‘yan bindiga 16 a wani rikici a kananan hukumomin Birnin Gwari da Chikun, sannan an lalata sansanoni sama da 100 da ‘yan ta’adda suka mamaye.

Sai dai Aruwan ya ci gaba da cewa a cikin wannan lokaci jami’an tsaro sun ceto mutane 74 da aka yi garkuwa da su.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ya kuma bayyana cewa, makaman da aka kama daga hannun ‘yan bindigar a cikin watanni shidan sun hada da, manyan bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK-47 guda saba’in da hudu, AK-49 guda daya da kuma bindigogi kirar 06 guda tara.

Sauran sun hada da bindigogi masu wuta guda hudu, bindigogin fanfo guda hudu, bindiga g3 daya, bindigu na gida guda goma sha shida da kuma harsashi guda 5,398.

Ya kuma bayyana cewa an kwato haramtattun abubuwa daga hannun wadanda ake zargin.

Ya ce adadin haramtattun abubuwan da aka kama sun kai kilogiram 2,759.891 na tabar wiwi da miyagun kwayoyi.

Ya kara da cewa an samu ci gaba sosai a hanyar Kaduna zuwa Abuja, inda ya ce kashe-kashe da garkuwa da mutane a hanyar Kaduna zuwa Abuja ya ragu matuka a kashi na uku, ya kara da cewa kokarin hadin gwiwar yana samun sakamako mai kyau.

Aruwan, wanda ya bayyana godiyarsa ga kwamandoji, hafsoshi da jami’an tsaro da suke aiki dare da rana don ganin an kyautata wa kowa, ya kuma bukaci jami’an tsaro da kada su yi kasa a gwiwa, wajen dakile hare-hare.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.