ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa Sojojin Da Suka Kashe ‘Yan Bindiga 152 Tare Da Lalata Sansani 100

by Sadiq
4 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 152 tare da lalata sansaninsu sama da 100 a karo na biyu da na uku a 2022.

Mista Samuel Aruwan, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin da yake gabatar da rahoton yanayin tsaro na kashi na biyu da na uku na shekarar 2022, ga gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai.

  • ‘Gaskiyar Lamari Game Da Zargin Amfani Da Sinadarin Mercury A Rigakafin Yara’
  • Xi Ya Yi Jawabi Ga Taron COP14 Kan Kiyaye Filaye Masu Dausayi

Aruwan ya ce dakarun kasa da ke kewayen jihar sun kashe ‘yan bindiga 152.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, an kashe ‘yan bindiga da dama a lokacin da aka kai farmaki ta sama kan sansanonin da aka gano, inda ya ce an kashe ‘yan bindiga 16 a wani rikici a kananan hukumomin Birnin Gwari da Chikun, sannan an lalata sansanoni sama da 100 da ‘yan ta’adda suka mamaye.

Sai dai Aruwan ya ci gaba da cewa a cikin wannan lokaci jami’an tsaro sun ceto mutane 74 da aka yi garkuwa da su.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Ya kuma bayyana cewa, makaman da aka kama daga hannun ‘yan bindigar a cikin watanni shidan sun hada da, manyan bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK-47 guda saba’in da hudu, AK-49 guda daya da kuma bindigogi kirar 06 guda tara.

Sauran sun hada da bindigogi masu wuta guda hudu, bindigogin fanfo guda hudu, bindiga g3 daya, bindigu na gida guda goma sha shida da kuma harsashi guda 5,398.

Ya kuma bayyana cewa an kwato haramtattun abubuwa daga hannun wadanda ake zargin.

Ya ce adadin haramtattun abubuwan da aka kama sun kai kilogiram 2,759.891 na tabar wiwi da miyagun kwayoyi.

Ya kara da cewa an samu ci gaba sosai a hanyar Kaduna zuwa Abuja, inda ya ce kashe-kashe da garkuwa da mutane a hanyar Kaduna zuwa Abuja ya ragu matuka a kashi na uku, ya kara da cewa kokarin hadin gwiwar yana samun sakamako mai kyau.

Aruwan, wanda ya bayyana godiyarsa ga kwamandoji, hafsoshi da jami’an tsaro da suke aiki dare da rana don ganin an kyautata wa kowa, ya kuma bukaci jami’an tsaro da kada su yi kasa a gwiwa, wajen dakile hare-hare.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.