• English
  • Business News
Sunday, September 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Za Ta Horas Da Ɗalibai 32,000 Sana’oin Hannu A Duk Shekara – Maiyaki

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 hours ago
in Labarai
0
Harin Bam: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Sake Ginin Garin Tudun Biri 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, ta sanar da shirinta na horas da kuma yaye dalibai 32,000 a duk shekara ta hannun Cibiyar Horas da Sana’o’i da Ƙwarewa da aka kafa kwanan nan.

 

Cibiyar wadda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar a watan Yuni na da rassan da aka tsara su da kyau a Rigachikun, Soba da Samarun Kataf. Rassan cibiyar sun samu kayan aiki na zamani domin samar da horo na dindindin, wanda zai ba da kwarewa ta zahiri da ta zamani da kuma ta duniya.

  • Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?
  • Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

Dalibai na iya yin rajista a cikin kowanne daga cikin fannoni 14 na sana’o’in da Hukumar Kula da Ilimin Fasaha ta Ƙasa (NBTE) ta amince da su, waɗanda suka haɗa da: Fenti da Kwalliya (POP/, Gini da Sanya Tiles da Bututun Ruwa (Plumbing), Kere-kere da Gyaran Katako Walda da Kera Karfe daq Sanya Wutar Lantarki da Kera Aluminium da Firiji da A/C da kuma Sanya Hasken Rana sai kuma Gyaran Kwamfuta , Girki da Kulawa da Baƙi da Ƙira da Dinkin Kaya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

Yayin da yake bayani kan muhimmancin wannan shiri, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya ce: “Wannan Cibiyar wata gagarumar alama ce ta kudurin Gwamnatin Jihar Kaduna na bunkasa koyon sana’o’i, karfafa matasa, da haɓaka tattalin arziki.

 

Yace An zaɓi fannonin sana’o’i 14 ne cikin hikima domin su magance manyan bukatun ƙwararrun ma’aikata a bangarorin gine-gine, makamashi, fasahar zamani (ICT), kula da baƙi, da harkokin ƙirƙira. Muna da yakinin cewa waɗanda suka kammala karatu a wannan Cibiyar ba kawai za su samu ayyukan yi ba ne, har ma za su zama masu dogaro da kai kuma su samar da dama ga wasu.”

 

Shima Shugaban Cibiyar, Malam Husaini Haruna Muhammad, ya jaddada muhimmancin da horon ke da shi wajen dacewa da bukatun kasuwanni da wuraren aiki: “Abin da muke mayar da hankali a kai shi ne samar da daliban da suka kammala karatu waɗanda suke da shirye-shiryen fuskantar kasuwa da wuraren aiki. Kashi 80% na horonmu yana kasancewa ne na aikace-aikace, wanda ke ba wa ɗalibai damar samun ƙwarewar rayuwa ta ainihi a fannonin da suka zaɓa. Wadannan ƙwarewar ba wai kawai sun dace da tattalin arzikin Najeriya ba ne, har ma suna da gasa a matakin duniya. Muna ƙarfafa ‘yan ƙasa musamman mata, masu nakasa da matasa masu rauni da su amfana da wannan dama.”

 

Tare da kayan aiki da ma’aikata masu ƙwarewa da aka tanada, cibiyar na da niyyar yaye ɗalibai 16,000 a zangon horo na farko, tare da nufin cimma burinta na yaye ɗalibai 32,000 a kowace shekara.

 

Yace Gwamnatin Jihar Kaduna na kira ga al’ummar jihar da ma wajenta da su yi amfani da wannan dama don samun ƙwarewa da za ta basu damar samun aiki, kafa nasu sana’a, da dogaro da kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

Next Post

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

Related

Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

3 hours ago
Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

5 hours ago
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai
Manyan Labarai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

7 hours ago
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC
Labarai

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

8 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

18 hours ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

23 hours ago
Next Post
Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

September 28, 2025
Harin Bam: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Sake Ginin Garin Tudun Biri 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Horas Da Ɗalibai 32,000 Sana’oin Hannu A Duk Shekara – Maiyaki

September 28, 2025
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

September 28, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Kano

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

September 28, 2025
Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

September 28, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

September 28, 2025
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

September 28, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.