ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

by Abba Ibrahim Wada
12 months ago
Haaland

A wannan sabuwar kakar da aka fara, babu gasar da aka ci kasuwar manyan ‘yan wasan gaba a nahiyar turai kamar kasar Ingila domin a Ingila ne idan ka cire Manchester City kusan duk manyan kungiyoyin gasar sun sayi dan wasan gaba.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta dauki Biktor Gyokeres daga Sporting Lisbon sai Manchester United wadda ta dauki Benjamis Sesko, ya yin da Newcastle United ta dauki ‘yan wasan gaba guda biyu da suka hada da Nick Woltemade da Yoanne Wissa.

  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira
  • Yadda Ake Hada Sushi

Mai kare kambu sannan wadda take jan ragamar gasar a wannan lokaci, Liberpool, ta dauki manyan ‘yan wasan gaba guda biyu da suka hada da Hugo Ekitike da Aledander Isak. Ita ma kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ‘yan wasan gaba guda biyu ta dauka, inda ta fara daukar Liam Delap daga Ipswich Town da Joao Pedro, dan Brazil, daga kungiyar Brighton Albion.

ADVERTISEMENT

Amma duk da haka matashin dan wasa Erling Haaland ya ci kwallaye 13 a kungiyar Manchester City da kasarsa ta Norway daga fara kakar wasa ta bana, har da wadda ya zura a ragar Arsenal ranar Lahadi a Premier League.

Kenan wasanni takwas jimilla ya buga kawo yanzu, masu sharhi suna ganin hakan na nufin zai iya lashe takalmin zinare a fagen cin kwallaye a nahiyar Turai da Premier League idan har aka ci gaba da tafiya a haka.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Haaland ya fara da zura kwallo biyu a raga a wasan da Manchester City ta caskara kungiyar kwallon kafa ta Wolberhampton 4-0 a gasar Premier League ranar 16 ga watan Agusta. Ya kuma ci kwallayen a minti na 34 da kuma a 61 a karawar da aka yi a filin wasa na Molineud a wasan makon farko a babbar gasar Ingila.

Sai dai dan wasan tawagar ta Norway bai ci kwallo ba a mako na biyu a wasan da Tottenham ta doke City 2-0 a Etihad, sai dai daga lokacin ya ci kwallaye a dukkan wasannin da ya buga na gaba. Ranar 31 ga watan Agusta, Manchester City ta yi rashin nasara 2-1 a gidan Brighton a wasan mako na uku a Premier League, Haaland ne ya fara cin kwallo tun kafin hutun rabin lokaci.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Brighton ta farke ta kuma kara ta biyu da ta kai ta hada maki ukun da take bukata.

Norway ta buga wasan sada zumunta da Finland ranar 4 ga watan Satumba, inda Norway ta yi nasara 1-0, kuma Haaland ne ya ci kwallon a bugun fenariti a minti na 17 da fara wasa. Daga nan Haaland ya zura biyar a ragar Moldoba lokacin da Norway ta sharara 11-1 a wasan neman shiga gasar cin kofin duniya, inda mai tsaron raga, Cristian Abram ya ce Haaland ya je ya bashi hakuri kan yawan kwallaye da Norway ta zura musu.

Da ya koma Ingila, bayan buga wasannin neman shiga gasar kofin duniya, Haaland ya zura kwallo biyu a ragar Manchester United a wasan hamayya a Premier League mako na hudu ranar 14 ga watan Satumba. Daga nan Manchester City ta fara buga Champions League wasan farko a cikin rukuni da doke Napoli 2-0 ranar 18 ga watan Satumba, inda Haaland ne ya fara cin kwallo da suka koma zagaye na biyu a filin wasa na Etihad.

Ranar Lahadi Haaland ya fara cin Arsenal kwallo a Premier League wasan mako na biyar, kuma na biyar da ya ci Arsenal a karawa ta bakwai, sannan kwallo ta 20 daga wasa 21 da ya ziyarci duk wata kungiyar kwallon kafa da take birnin Landan.

Kenan Haaland ya ci kwallo shida a Premier League, sannan bakwai a Manchester City har da wadda ya zura a ragar Napoli a Champions League, jimilla ya ci 13 a karawa takwas a kungiya da kasarsa. Wannan kakar Haaland bai fara da kokari ba duk da cin kwallo shida a wasa biyar a Premier League tun bayan da ya koma Manchester City a kakar wasa ta 2022 zuwa 2023.

A kakarsa ta farko ya zura kwallo tara a raga a wasa biyar da fara kakar gasar firimiya ta Ingila, sai kuma ya ci bakwai a wasa biyar da fara kakar wasa ta 2023 zuwa 2024. Amma a bara 10 ya zura a raga da fara wasan Premier League biyar har da uku rigis da ya ci Ipswich Town da kuma West Ham United.

A kakar nan ya zura kwallo biyu a raga a wasa shi ne a Wolberhampton a Molineud a Premier League da kuma Manchester United a wasan hamayya a filin wasa na Etihad da ke birnin Manchester. Kwallo biyar da Haaland ya sharara a ragar Moldoba ya yi kan-kan-kan da tarihin da ya kafa a baya a Manchester City a fafatawa da RB Leipzig a 2022 zuwa 2023 Champions League da wasa da Luton a FA Cup a 2023 zuwa 2024.

Karo 26 yana cin kwallo uku rigis a raga a tarihi, kuma na biyar a tawagar Norway. Ya ci kwallo uku rigis a Manchester City da karo uku yana zura uku rigis a raga a Norway tun daga lokacin da ya koma buga wasa a Etihad. Ranar 10 ga watan Mayun 2022, Manchester City ta sanar da sayen Erling Haaland daga Borussia Dortmund.

Kofunan Da Haaland Ya Lashe

Red Bull Salzburg

Austrian Bundesliga: 2018–19, Austrian Cup: 2018–19, Borussia Dortmund

DFB-Pokal: 2020–21

Manchester City

Premier League: 2022–23, 2023–24. FA Cup: 2022–23, FA Community Shield: 2024

UEFA Champions League: 2022–23, UEFA Super Cup: 2023.

Norway U17

Syrenka Cup: 2016,

Haaland
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Kano

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.