Gwamnatin Jihar Kano, ta sassauta dokar hana fita daga karfe 8 na safe zuwa karfe 2 na rana a jihar.
Kwamishinan Yada Labarai na jihar, Baba Halilu Ɗantiye ne, ya bayyana haka ga manema labarai a Kano.
- Wakilin CMG Ya Zanta Da Shugaban Kasar Timor-Leste
- An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano
Sanarwar, ta bayyana cewa sassaucin dokar zai fara daga gobe Lahadi da misalin karfe 8 na safe zuwa ƙarfe 2 na rana don jama’a su samu su gudanar da harkokinsu a tsakanin wannan lokacin kafin komai ya daidaita.
Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin ta sanya dokar hana fita biyo bayan tashe-tashen hankula da aka samu a lokacin zanga-zangar yunwa a ranar Alhamis a jihar.
An fara zanga-zangar ne a fadin Nijeriya don nuna fushi kan halin da kasar ke ciki game da tabarbarewar tattalin arziki da kuma tashin gwauron zabin kayan abinci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp