ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kano

Ana fargabar mutane da dama sun mutu, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata, sakamakon wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan daba da jami’an tsaro a Jihar Kano.

Yankunan da lamarin ya shafa sun hada da Rijiyar Lemo, Kurna zuwa Bachirawa a karamar hukumar Fagge, Kofar Nassarawa a karamar hukumar Birni, da Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni.

  • Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi A Ranar Lahadi
  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

A cewar wasu shaidun gani da ido, arangamar ta fara ne a lokacin da wasu matasa suka bijirewa dokar hana fita da aka sanya a jihar tare da fitowa kan tituna, inda suka ci gaba da zanga-zangar da ta rikide zuwa tashin hankali a Kano.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin Rijiyar Lemo mai suna Abdulkadir Musa ya ce, “Akalla mutane takwas ne aka harbe a yankinmu da suka hada da mata da yara. Yanzu haka wata tsohuwa ta mutu tare da wasu uku, yayin da da dama suka samu munanan raunuka.

“A gaskiya abin da ya faru shi ne, kun san har yanzu dokar hana fita tana nan, don haka mutane suka bijirewa hakan suka fito suna zanga-zanga. A lokacin ne jami’an tsaro suka fara kai farmaki, suna kokarin tarwatsa su, kuma ana cikin haka ne sai da suka yi harbin domin su tarwatsa masu zanga-zangar.”

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Wani mazaunin garin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya ce ‘yan daban da suka fake da zanga-zangar yunwar, sun yi yunkurin fasa shaguna, ciki har da shagon Rufaida Yoghourt.

Ya ce jami’an tsaro sun tarwatsa ’yan daban, inda daga nan ne suka fara jifan su da duwatsu.

An bayyana cewa wani jami’in ‘yan sanda ya ji rauni a yayin arangamar, ko da yake ba a tantance shi ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Mutanen da harsashi ya rutsa da su yanzu haka suna samun kulawar likitoci a asibitin Salamatu.

Wata mai amfani da shafukan sada zumunta, Aiha K Nass, ta wallafa, “Muna nan muna makokin kakarmu; ‘yan sanda sun harbe yayana Aliyu. Yanzu haka ya mutu.”

Wani mai amfani da shafukan sada zumunta, Omar Khalid Saleh, ya rubuta cewa, “’Yan sanda a Kano sun mayar da zanga-zangar lumana zuwa wani abu daban. Me ya sa ake harbe-harbe da kashe-kashe? Kuna gayyatar matsala. Sun harbe wannan matashi ne, kuma ya mutu nan take a Kofar Nasarawa, cikin birnin Kano. #EndBadGovernance A Nijeriya #KarshenYanSanda.”

Masu zanga-zangar sun fito kan titin Zariya da ke kan Unguwa Uku amma kuma jami’an tsaro sun tarwatsa su.

An jibge karin jami’an tsaro domin dakile zirga-zirga a Kurna Asabe, kusa da Barikin Sojoji na Bukavu.

Kokarin jin ta bakin kakakin ‘yansandan jihar, ya ci tura domin har zuwa lokacin hada wannan rahoto, SP Abudullahi Haruna Kiyawa bai daga waya ba.

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.