ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kano

Ana fargabar mutane da dama sun mutu, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata, sakamakon wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan daba da jami’an tsaro a Jihar Kano.

Yankunan da lamarin ya shafa sun hada da Rijiyar Lemo, Kurna zuwa Bachirawa a karamar hukumar Fagge, Kofar Nassarawa a karamar hukumar Birni, da Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni.

  • Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi A Ranar Lahadi
  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

A cewar wasu shaidun gani da ido, arangamar ta fara ne a lokacin da wasu matasa suka bijirewa dokar hana fita da aka sanya a jihar tare da fitowa kan tituna, inda suka ci gaba da zanga-zangar da ta rikide zuwa tashin hankali a Kano.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin Rijiyar Lemo mai suna Abdulkadir Musa ya ce, “Akalla mutane takwas ne aka harbe a yankinmu da suka hada da mata da yara. Yanzu haka wata tsohuwa ta mutu tare da wasu uku, yayin da da dama suka samu munanan raunuka.

“A gaskiya abin da ya faru shi ne, kun san har yanzu dokar hana fita tana nan, don haka mutane suka bijirewa hakan suka fito suna zanga-zanga. A lokacin ne jami’an tsaro suka fara kai farmaki, suna kokarin tarwatsa su, kuma ana cikin haka ne sai da suka yi harbin domin su tarwatsa masu zanga-zangar.”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Wani mazaunin garin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya ce ‘yan daban da suka fake da zanga-zangar yunwar, sun yi yunkurin fasa shaguna, ciki har da shagon Rufaida Yoghourt.

Ya ce jami’an tsaro sun tarwatsa ’yan daban, inda daga nan ne suka fara jifan su da duwatsu.

An bayyana cewa wani jami’in ‘yan sanda ya ji rauni a yayin arangamar, ko da yake ba a tantance shi ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Mutanen da harsashi ya rutsa da su yanzu haka suna samun kulawar likitoci a asibitin Salamatu.

Wata mai amfani da shafukan sada zumunta, Aiha K Nass, ta wallafa, “Muna nan muna makokin kakarmu; ‘yan sanda sun harbe yayana Aliyu. Yanzu haka ya mutu.”

Wani mai amfani da shafukan sada zumunta, Omar Khalid Saleh, ya rubuta cewa, “’Yan sanda a Kano sun mayar da zanga-zangar lumana zuwa wani abu daban. Me ya sa ake harbe-harbe da kashe-kashe? Kuna gayyatar matsala. Sun harbe wannan matashi ne, kuma ya mutu nan take a Kofar Nasarawa, cikin birnin Kano. #EndBadGovernance A Nijeriya #KarshenYanSanda.”

Masu zanga-zangar sun fito kan titin Zariya da ke kan Unguwa Uku amma kuma jami’an tsaro sun tarwatsa su.

An jibge karin jami’an tsaro domin dakile zirga-zirga a Kurna Asabe, kusa da Barikin Sojoji na Bukavu.

Kokarin jin ta bakin kakakin ‘yansandan jihar, ya ci tura domin har zuwa lokacin hada wannan rahoto, SP Abudullahi Haruna Kiyawa bai daga waya ba.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.