• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Horar Da Jaruman Kannywood 100 A Kan Harkokin Fim Da Kasuwanci

by Rabilu Sanusi Bena
12 months ago
in Nishadi
0
Rashin Amsa Gayyata Ya Sa Muka Dakatar Da Khadija Mai Numfashi —Abba El Mustapha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano za ta horar da jarumai 100 na masana’antar Kannywood kan harkar fim da kasuwanci kamar yadda shugaban hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano Abba El Mustapha ya bayyana wa ‘yan jarida.

Alhaji Abba El-mustapha ya jaddada akkawuran gwamnatin Engr. Abba Kabir Yusuf inda ya ce zai wadata masana’antar fina-finan kannywood da dabarun zamani wajen shirya fina-finai.

  • Ambaliya: Uwargidan Gwamnan Yobe Ta Janjanta Wa Al’ummar Maiduguri 
  • Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

Abba El-Mustapha ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da fom 100 na aikace-aikace ga ’yan masana’antar Kannywood na shirin horarwa na tsawon watanni biyu kan harkar fim da kasuwanci, wanda Cibiyar Fina-Finai ta Jihar Kano za ta gudanar.

Abba El-mustapha ya bayyana cewa shirin wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Jihar Kano ke yi na bunkasa fasahar ‘yan masana’antar Kannywood, da samar musu da dabarun shirya fina-finai na zamani, da ka’idojin da’a, da dabarun kasuwanci don bunkasa dogaro da kai.

Ya ci gaba da cewa shirin na da nufin baiwa mahalarta taron ilimi da kayan aikin da suka dace don samun nasara a harkar fim a lokuta masu zuwa,ya kuma bukaci daukacin mahalarta taron da su yi amfani da wannan dama mai kima da gwamnatin jihar Kano ta ba su, tare da jaddada muhimmancin yin fim din.

Labarai Masu Nasaba

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Horar da su don ciyar da sana’o’insu gaba da kuma ba da gudummawa ga ci gaban masana’antar fim ta cikin gida.

Manufar wannan horon ita ce fadakar da masu shirya fina-finai namu da ayyukan zamani da ka’idojin da’a, ta yadda za su kasance masu dogaro da kai da samun nasara a harkokinsu,” in ji Abba El-mustapha.

A karshe ya yaba da gagarumin goyon baya da hadin kai daga gwamnati wajen aiwatar da shirin da sauran tsare-tsare da ke amfanar masana’antu.

A nasa jawabin shugaban kungiyar masu harkar fim ta Jihar Kano, Malam Alhassan Kwalle, ya bayyana matukar godiya ga gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na inganta masana’antar a jihar.

Ya ce muna godiya ga Gwamna Yusuf da ya dauke mu a matsayin wadanda suka cancanta,da kuma wannan damar don inganta kwarewarmu kuma daga karshe ina kyautata zaton da wannan horo da zamu samu,muna da tabbacin cewa mambobinmu za su iya yin gogayya da takwarorinsu na duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiKannywoodkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Tagomashi A Watan Augusta

Next Post

Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

Related

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 days ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 week ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

3 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Next Post
Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.