• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Horar Da Jaruman Kannywood 100 A Kan Harkokin Fim Da Kasuwanci

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano za ta horar da jarumai 100 na masana’antar Kannywood kan harkar fim da kasuwanci kamar yadda shugaban hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano Abba El Mustapha ya bayyana wa ‘yan jarida.

Alhaji Abba El-mustapha ya jaddada akkawuran gwamnatin Engr. Abba Kabir Yusuf inda ya ce zai wadata masana’antar fina-finan kannywood da dabarun zamani wajen shirya fina-finai.

  • Ambaliya: Uwargidan Gwamnan Yobe Ta Janjanta Wa Al’ummar Maiduguri 
  • Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

Abba El-Mustapha ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da fom 100 na aikace-aikace ga ’yan masana’antar Kannywood na shirin horarwa na tsawon watanni biyu kan harkar fim da kasuwanci, wanda Cibiyar Fina-Finai ta Jihar Kano za ta gudanar.

Abba El-mustapha ya bayyana cewa shirin wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Jihar Kano ke yi na bunkasa fasahar ‘yan masana’antar Kannywood, da samar musu da dabarun shirya fina-finai na zamani, da ka’idojin da’a, da dabarun kasuwanci don bunkasa dogaro da kai.

Ya ci gaba da cewa shirin na da nufin baiwa mahalarta taron ilimi da kayan aikin da suka dace don samun nasara a harkar fim a lokuta masu zuwa,ya kuma bukaci daukacin mahalarta taron da su yi amfani da wannan dama mai kima da gwamnatin jihar Kano ta ba su, tare da jaddada muhimmancin yin fim din.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Horar da su don ciyar da sana’o’insu gaba da kuma ba da gudummawa ga ci gaban masana’antar fim ta cikin gida.

Manufar wannan horon ita ce fadakar da masu shirya fina-finai namu da ayyukan zamani da ka’idojin da’a, ta yadda za su kasance masu dogaro da kai da samun nasara a harkokinsu,” in ji Abba El-mustapha.

A karshe ya yaba da gagarumin goyon baya da hadin kai daga gwamnati wajen aiwatar da shirin da sauran tsare-tsare da ke amfanar masana’antu.

A nasa jawabin shugaban kungiyar masu harkar fim ta Jihar Kano, Malam Alhassan Kwalle, ya bayyana matukar godiya ga gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na inganta masana’antar a jihar.

Ya ce muna godiya ga Gwamna Yusuf da ya dauke mu a matsayin wadanda suka cancanta,da kuma wannan damar don inganta kwarewarmu kuma daga karshe ina kyautata zaton da wannan horo da zamu samu,muna da tabbacin cewa mambobinmu za su iya yin gogayya da takwarorinsu na duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Next Post
Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Kannywood

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.