ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Horar Da Jaruman Kannywood 100 A Kan Harkokin Fim Da Kasuwanci

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano za ta horar da jarumai 100 na masana’antar Kannywood kan harkar fim da kasuwanci kamar yadda shugaban hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano Abba El Mustapha ya bayyana wa ‘yan jarida.

Alhaji Abba El-mustapha ya jaddada akkawuran gwamnatin Engr. Abba Kabir Yusuf inda ya ce zai wadata masana’antar fina-finan kannywood da dabarun zamani wajen shirya fina-finai.

  • Ambaliya: Uwargidan Gwamnan Yobe Ta Janjanta Wa Al’ummar Maiduguri 
  • Me Ya Haddasa Cacar Baki Tsakanin Kwankwaso Da PDP?

Abba El-Mustapha ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da fom 100 na aikace-aikace ga ’yan masana’antar Kannywood na shirin horarwa na tsawon watanni biyu kan harkar fim da kasuwanci, wanda Cibiyar Fina-Finai ta Jihar Kano za ta gudanar.

ADVERTISEMENT

Abba El-mustapha ya bayyana cewa shirin wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Jihar Kano ke yi na bunkasa fasahar ‘yan masana’antar Kannywood, da samar musu da dabarun shirya fina-finai na zamani, da ka’idojin da’a, da dabarun kasuwanci don bunkasa dogaro da kai.

Ya ci gaba da cewa shirin na da nufin baiwa mahalarta taron ilimi da kayan aikin da suka dace don samun nasara a harkar fim a lokuta masu zuwa,ya kuma bukaci daukacin mahalarta taron da su yi amfani da wannan dama mai kima da gwamnatin jihar Kano ta ba su, tare da jaddada muhimmancin yin fim din.

LABARAI MASU NASABA

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Horar da su don ciyar da sana’o’insu gaba da kuma ba da gudummawa ga ci gaban masana’antar fim ta cikin gida.

Manufar wannan horon ita ce fadakar da masu shirya fina-finai namu da ayyukan zamani da ka’idojin da’a, ta yadda za su kasance masu dogaro da kai da samun nasara a harkokinsu,” in ji Abba El-mustapha.

A karshe ya yaba da gagarumin goyon baya da hadin kai daga gwamnati wajen aiwatar da shirin da sauran tsare-tsare da ke amfanar masana’antu.

A nasa jawabin shugaban kungiyar masu harkar fim ta Jihar Kano, Malam Alhassan Kwalle, ya bayyana matukar godiya ga gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na inganta masana’antar a jihar.

Ya ce muna godiya ga Gwamna Yusuf da ya dauke mu a matsayin wadanda suka cancanta,da kuma wannan damar don inganta kwarewarmu kuma daga karshe ina kyautata zaton da wannan horo da zamu samu,muna da tabbacin cewa mambobinmu za su iya yin gogayya da takwarorinsu na duniya.

Kannywood
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Buƙaci A Naɗa Kwamiti Domin Warware Matsalolin Hukumar
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

MASU ALAKA

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84
Nishadi

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

September 16, 2026
Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Next Post
Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai

Matatar Dangote Za Ta Ƙara Yawan Ma’aikata Da Samar Da Mai

September 18, 2026
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Binciken Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

September 18, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Zanga-Zanga Ta Ɓarke A Minna

September 18, 2026
ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

ICPC Ta Yi Wa Dan Takarar APC A Ekiti Titsiye Kan Zargin Badakalar Kuɗi

September 18, 2026
Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Abubuwa 12 Da Ya Kamata A Sani Kan Abin Da Aka Aika Wa Majalisun Jihohi

September 18, 2026
Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026
Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

September 17, 2026
U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.