• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kasar Sin Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Ta Hanyar Ingiza Samun Wadata Ba Tare Da Barin Kowa A Baya Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gwamnatin Kasar Sin Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Ta Hanyar Ingiza Samun Wadata Ba Tare Da Barin Kowa A Baya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abin dake shaida wadata da karfin wata kasa shi ne karfinta na kawar da talauci, kuma shaidar karfin wata gwamnati shi ne matakan da ta dauka don rage gibin dake tsakanin mawadata da matalauta.

Tabbatar da samun wadata ba tare da barin kowa a baya ba, daya ne daga cikin wasu muhimman abubuwa dake cikin tsarin mulki na gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin. Mawadata su taimakawa matalauta wajen fita daga talauci, wata hanya ce mai kyau ta tabbatar da wannan buri.

  • Gidauniyar Masari Ta Tallafa Wa Marasa Karfi A Jihar Katsina

Ni ne na yi sa’a sosai, saboda iyali na daya ne daga cikin iyalan da suka samu matsaikaciyar wadata a matakin farko, amma a wancan lokaci, wato waje yau shekaru 30 da suka gabata, a lokacin da nake karatu a makarantar firamare, ban san cewa akwai wasu mutane da suke fama da talauci mai tsanani a yankunan karkara ba.

Kasar Sin

Wata rana, makarantar da nake karatu ta kai mu wani kauye, don sanin yadda manoman kauye suke da zama, sannan mu ba su wasu kayayyakin jin kai.

Labarai Masu Nasaba

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Wanda na baiwa taimako shi ne wani yaro mai shekaru daidai da nawa, ya kuma gaya min cewa, a baya ya dauka cewa, ba zai iya kammala karatun firamare ba sai dai ya nemi wani aikin yi domin taimakawa iyayensu fama da talauci, daga baya gwamnatin wurin ta ba iyalinsa wasu kudin tallafi, shi ya sa ya koma makaranta, zaman rayuwar gidansa ma ya samu kyautatu.

A waccan lokaci, ni karamar yarinya ce, ba ni da karfin taimaka masa, amma na san cewa, ina da nauyin dake bisa wuya na a nan gaba, wato dole ne na taimakawa sauran mutane dake fama da talauci idan na samu arziki.

Wani dan jarida ya ga ni da wancan yaro muna rubutawa juna adireshenmu, sai ya tambaye ni dalili, na ba shi amsa cewa, na sa niyyar ci gaba da taimake shi nan gaba. Na yi imanin cewa, duk daliban da suka halarci wannan aikin da makarantarmu ta tsara, za su fahimci ma’anar samun arziki tare, kuma za su sauke nauyin dake wuyansu na taimakawa wadanda suke bukata nan gaba.

Kasar Sin
Gudanar da irin wannan aiki a cikin makaranta, hanya daya ce daga cikin matakan da gwamnatocin matakai daban daban na kasar Sin su kan dauka, na ilmantar da yara sanin taimakawa duk wanda yake bukata.

Masanin kasar Birtaniya Martin Jacques ya taba nuna cewa, babban sauyin da Sin take saukewa ya wuce tunanin mutanen yammacin duniya. Martin Jacques ya fadi gaskiya, tun lokacin kafuwar jamhuriyyar jama’ar kasar Sin zuwa lokacin kaddamar da manufar yin kwaskwarima a gida da bude kofa ga waje, har zuwa sabon zamani na gina zaman al’ummar gurguzu mai sigar halayen kasar Sin, gwamantin kasar Sin ta kan sanya moriyar fararen hula a gaban kome, ba ta taba mantawa da kowa ba.

Kasar Sin ta samu ci gaba da ba a taba ganin irinsa a tarihi ba, wannan shi ne niyyar JKS ta samarwa dukkan jama’arta zaman rayuwa mai arziki.

A ganin Martin Jacques, Sin tana daidaita matsalar rashin adalci ta hanyar aiwatar da manufar samun arzik tare, abin da manyan kasashen yamma har yanzu ba su cimma nasara ba tukuna. Kawar da rashin daidaito da rage gibin mawadata da matalauta nauyi ne dake wuyan duk wata gwamnati, kuma ya zama dole ga kowace gwamnati.

Amma lokacin da gwamnatin kasar Sin ta aiwatar da irin wannan mataki, wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma sun shafa mata bakin fenti wai cewa, gwamnatin Sin na kara karfin mallaka.

Idan gwamnatoci biyu da suke kasancewa a gaban jama’a a lokaci daya, wata daga cikinsu ta yi alwashi kawai a maimakon kokarin cika alkawari, amma wata daban ta kan dauki nagartattun matakai wajen kawar da talauci, da ba da taimako ga wadanda suke domin kokarin cika alkawarinta, ku gaya mana wace kuke so ko kuke bukata? (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Gudanar Da Maulidin Alhaji Bala Mai Salla Karo Na 21

Next Post

‘Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

Related

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

1 hour ago
Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki
Daga Birnin Sin

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

9 hours ago
Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

10 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

11 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

12 hours ago
Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba
Daga Birnin Sin

Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

13 hours ago
Next Post
‘Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

'Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Manyan Jami’an ‘Yansanda 150 Ke Fuskantar Kwamitin Ladabtarwa

July 18, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

July 18, 2025
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

July 18, 2025
Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

July 17, 2025
Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar ÆŠantata

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar ÆŠantata

July 17, 2025
Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

July 17, 2025
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

July 17, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

July 17, 2025
Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

July 17, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.