• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kasar Sin Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Ta Hanyar Ingiza Samun Wadata Ba Tare Da Barin Kowa A Baya Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gwamnatin Kasar Sin Ta Sauke Nauyin Dake Wuyanta Ta Hanyar Ingiza Samun Wadata Ba Tare Da Barin Kowa A Baya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abin dake shaida wadata da karfin wata kasa shi ne karfinta na kawar da talauci, kuma shaidar karfin wata gwamnati shi ne matakan da ta dauka don rage gibin dake tsakanin mawadata da matalauta.

Tabbatar da samun wadata ba tare da barin kowa a baya ba, daya ne daga cikin wasu muhimman abubuwa dake cikin tsarin mulki na gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin. Mawadata su taimakawa matalauta wajen fita daga talauci, wata hanya ce mai kyau ta tabbatar da wannan buri.

  • Gidauniyar Masari Ta Tallafa Wa Marasa Karfi A Jihar Katsina

Ni ne na yi sa’a sosai, saboda iyali na daya ne daga cikin iyalan da suka samu matsaikaciyar wadata a matakin farko, amma a wancan lokaci, wato waje yau shekaru 30 da suka gabata, a lokacin da nake karatu a makarantar firamare, ban san cewa akwai wasu mutane da suke fama da talauci mai tsanani a yankunan karkara ba.

Kasar Sin

Wata rana, makarantar da nake karatu ta kai mu wani kauye, don sanin yadda manoman kauye suke da zama, sannan mu ba su wasu kayayyakin jin kai.

Labarai Masu Nasaba

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Wanda na baiwa taimako shi ne wani yaro mai shekaru daidai da nawa, ya kuma gaya min cewa, a baya ya dauka cewa, ba zai iya kammala karatun firamare ba sai dai ya nemi wani aikin yi domin taimakawa iyayensu fama da talauci, daga baya gwamnatin wurin ta ba iyalinsa wasu kudin tallafi, shi ya sa ya koma makaranta, zaman rayuwar gidansa ma ya samu kyautatu.

A waccan lokaci, ni karamar yarinya ce, ba ni da karfin taimaka masa, amma na san cewa, ina da nauyin dake bisa wuya na a nan gaba, wato dole ne na taimakawa sauran mutane dake fama da talauci idan na samu arziki.

Wani dan jarida ya ga ni da wancan yaro muna rubutawa juna adireshenmu, sai ya tambaye ni dalili, na ba shi amsa cewa, na sa niyyar ci gaba da taimake shi nan gaba. Na yi imanin cewa, duk daliban da suka halarci wannan aikin da makarantarmu ta tsara, za su fahimci ma’anar samun arziki tare, kuma za su sauke nauyin dake wuyansu na taimakawa wadanda suke bukata nan gaba.

Kasar Sin
Gudanar da irin wannan aiki a cikin makaranta, hanya daya ce daga cikin matakan da gwamnatocin matakai daban daban na kasar Sin su kan dauka, na ilmantar da yara sanin taimakawa duk wanda yake bukata.

Masanin kasar Birtaniya Martin Jacques ya taba nuna cewa, babban sauyin da Sin take saukewa ya wuce tunanin mutanen yammacin duniya. Martin Jacques ya fadi gaskiya, tun lokacin kafuwar jamhuriyyar jama’ar kasar Sin zuwa lokacin kaddamar da manufar yin kwaskwarima a gida da bude kofa ga waje, har zuwa sabon zamani na gina zaman al’ummar gurguzu mai sigar halayen kasar Sin, gwamantin kasar Sin ta kan sanya moriyar fararen hula a gaban kome, ba ta taba mantawa da kowa ba.

Kasar Sin ta samu ci gaba da ba a taba ganin irinsa a tarihi ba, wannan shi ne niyyar JKS ta samarwa dukkan jama’arta zaman rayuwa mai arziki.

A ganin Martin Jacques, Sin tana daidaita matsalar rashin adalci ta hanyar aiwatar da manufar samun arzik tare, abin da manyan kasashen yamma har yanzu ba su cimma nasara ba tukuna. Kawar da rashin daidaito da rage gibin mawadata da matalauta nauyi ne dake wuyan duk wata gwamnati, kuma ya zama dole ga kowace gwamnati.

Amma lokacin da gwamnatin kasar Sin ta aiwatar da irin wannan mataki, wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma sun shafa mata bakin fenti wai cewa, gwamnatin Sin na kara karfin mallaka.

Idan gwamnatoci biyu da suke kasancewa a gaban jama’a a lokaci daya, wata daga cikinsu ta yi alwashi kawai a maimakon kokarin cika alkawari, amma wata daban ta kan dauki nagartattun matakai wajen kawar da talauci, da ba da taimako ga wadanda suke domin kokarin cika alkawarinta, ku gaya mana wace kuke so ko kuke bukata? (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Gudanar Da Maulidin Alhaji Bala Mai Salla Karo Na 21

Next Post

‘Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

Related

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma
Daga Birnin Sin

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

6 hours ago
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

8 hours ago
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 
Daga Birnin Sin

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

10 hours ago
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci
Daga Birnin Sin

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

12 hours ago
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

20 hours ago
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

21 hours ago
Next Post
‘Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

'Yan Daba Sun Farmaki Mai Taimaka Wa Ganduje Na Musamman A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya NaÉ—a Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.