• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayar da umarnin rufe makarantu 32 na gaba da sakandare masu zaman kansu da ke aiki ba tare da lasisi ko sahalewar hukumomin da ke kula da ilimi ba a jihar.

Kwamishinan Ilimi na Manyan Makarantu, Fasaha da Sana’o’i, Dr. Muhammad Isah Kankara, ne ya bayyana hakan yayin kare kasafin kuɗin ma’aikatarsa na shekarar 2026 a gaban kwamiti ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan tsare-tsare da tattalin arziƙi, Malik Anas, a Katsina.

  • Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?
  • Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Dr. Kankara ya ce binciken ma’aikatar ya gano cewa da dama daga cikin makarantun masu zaman kansu suna gudanar da aiki ne ba bisa ƙa’ida ba, ba tare da cika ƙa’idojin ƙasa ba.

Ya bayyana cewa wannan mataki ya zama dole domin kare ɗalibai da tabbatar da ingancin ilimi a fadin jihar.

“Bincikenmu ya nuna cewa wasu makarantun masu zaman kansu suna aiki ne ba tare da amincewar hukumomin da suka dace ba,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Kwamishinan ya amince cewa rufe makarantun ya shafi kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR) da ake sa ran samu a shekarar 2026, domin da yawa daga cikin makarantun da aka rufe suna taka muhimmiyar rawa wajen samar da kuɗaɗen shiga ga ma’aikatar.

“Adadin kuɗaɗen shiga zai ragu a bana saboda yawancin waɗannan makarantun da aka dakatar suna cikin waɗanda ke taimaka mana wajen samar da kuɗi. Za mu iya dawo da su ne kawai idan suka cika sharuddan da doka ta tanada,” in ji Kankara.

A yayin zaman, shugaban kwamitin kasafin kuɗi, Malik Anas, ya umarci ma’aikatar da ta gabatar da cikakken jerin makarantun da ke da lasisi da waɗanda ba su da shi, tare da hasashen kudaden shiga daga kowacce.

Dr. Kankara ya bayyana cewa ma’aikatar tana tattara bayanan da ake buƙata kuma za ta mika cikakken rahoto nan ba da jimawa ba.

Ya ƙara da cewa makarantu guda bakwai (7) kawai daga cikin 39 masu zaman kansu ne aka tabbatar da sahihancinsu kuma suna ci gaba da aiki bayan wannan rufe-rufe.

Kwamitin ya yaba wa ma’aikatar bisa tsaurara dokoki don tabbatar da bin ƙa’idoji, tare da umartar ta da ta kawo sabbin bayanai kafin kasafin shekara mai zuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya - TRCN

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Katsina

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.