• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayyana Asabar din kowane jarshe wata a matsayin ranar tsaftar muhalli a jihar.

Gwamnan, ya bayyana haka ne wajen kaddamar da shirin tsaftar muhalli ta kowace karshe wata a jihar.

  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas
  • Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Gwamnan wanda mataimakinsa, Sanata Umar Abubakar Tafida ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yanke shawarar sake bullo da kuma karfafa shirin tsaftacce muhalli na wata ne saboda muhimmancinsa ga lafiyar jama’ar.

“Tsaftar muhalli da ruwan sha na da matukar muhimmanci ga jin dadin jama’a don rage cututtukan iska da na ruwa,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Gwamnatina za ta ci gaba da kula da harkokin kiwon lafiya a Jihar Kebbi, a koda yaushe domin tabbatar da cewa al’ummarmu sun kasance ‘yan jiha masu koshin lafiya kuma masu amfani cikin al’umma”.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Gwamnan ya ja kunnen jama’a da kada su rika sanya kansu cikin hatsari ta hanyar kazantar muhalli don gujewa cututtuka.

Da yake jawabinsa tun daga farko, Kwamishinan Ma’aikatar Tsaftar Muhalli, Alhaji Musa Muhammad Tungulawa, ya ce gwamnan ya umarci ma’aikatar da ta ci gaba da gudanar da gangamin tsaftace muhalli da wayar da kan jama’a don samun nasara.

“A ranar Asabar din karshe na kowane wata, za a gudanar da atisayen ne a babban birnin jihar, Birnin Kebbi, da kuma dukkan kananan hukumomin 21 na jihar,” in ji shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamna Nasir Idris ya ba da fifiko kan harkokin muhalli da kuma samun cikakkiyar tsafta a tsakanin ‘yan jihar.

Sarkin Gwandu, Alhaji Muhammadu Iliyasu Bashar, ya yaba wa gwamnan jihar kan matakin da ya dauka na tabbatar da tsaftar muhalli a jihar.

Sarkin ya umarci jama’a da su kasance masu biyayya da addu’a domin samun nasarar gwamnatin.

“Yin biyayya ga shugabanni yana da su yi aiki, yayin da shugabanci nagari ke ba jama’a kuzari don samun ingantacciyar rayuwa, wasu jihohi da masarautu a wasu wurare suna cikin mawuyacin hali, jihar Kebbi tana cikin kwanciyar hankali da tsaro mai kyau mu ci gaba da zaman lafiya da juna”, in ji Sarkin Gwandu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Kebbi

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.