ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

by Abubakar Abba
2 years ago
World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

World Bank on glass building. Mirrored sky and city modern facade. Global capital, business, finance, economy, banking and money concept 3D rendering animation.

Gwamnatin tarayya da Cibiyar Aikin Noma (IITA) da Bankin Duniya da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin aikin no-ma, sun ayyana kudirinsu na yin hadaka mai karfi a kan aikin noma wanda ke tattare da fasahar zamani.

Sun ayyana yin hakan ne, domin kawo karshen matsalar rashin amfani da fasahar zamani a fadin wannan kasa da kuma Na-hiyar Afirka baki-daya.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Kotun Koli Ta Bai Wa Jihohi 36 Kwana 7 Su Kare Kansu
  • Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi

Har ila yau, wannan kuduri na kunshe ne sakamakon wata ganawa da a aka yi tsakanin Mataimakin Shugaban Kasa, Sana-ta Kashim Shettima da wata tawaga da ta zo daga Cibiyar IITA da Bankin Duniya da kuma Cibiyar Gudanar da Bincken Tsarin Abinci ta Kasa da Kasa (IFPRI).

ADVERTISEMENT

Kazalika, Mataimakin Shugaban Kasar; a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar ya ce; an yi wannan ganawa ce, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.

Jawabin Shettima a wajen ganawar ya bayyana cewa, shirin zai mayar da hankali ne kan yadda za a kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Mataimakin ya ce, Cibiyar IITA ta kai matsayin da za ta taimaka wa ba Nijeriya kadai ba, har da ma dukkanin daukacin Nahiyar Afirka, ta yadda za a kara saita tsarin aikin noma da zai iya ju-rewa kowane irin sauyin yanayi tare da kara inganta Irin noma.

Haka zalika, ya yi nuni da cewa; Cibiyar IITA wadda aka kafa ta a shekarar 1967, ta jima tana bayar da gudunmawa ga wannan fanni na aikin noma a Nijeriya, sannan ya kara da cewa; har yanzu muna bukatar wannan gudunmawa tata.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa; nan da 2050, Nijeriya za ta kasance kasa ta uku cikin mafi yawan al’umma a doron kasa.

Ya sanar da cewa, Nahiyar Afirka na fusakantar kalubalen fari, sauyin yanayi da kuma kalubalen rashin tsaro, inda ya kara da cewa, fannin aikin noma na kasar nan na matukar fusakantar koma baya.
Har wa yau, Shettima ya yi kira ga Cibiyar ta IITA, da ta karfafa wannan hadaka, musamman domin samun damar zuba jari a fannin aikin noma ta fuskar kasuwanci.

Sannan kuma, ya bukaci cibiyar ta taimaka wa Nijeriya da ingantaccen Irin shuka na Masara da sauran amfanin gona, musamman Rogo.

Daga nan kuma, ya yaba wa IITA kan yunkurinta na samar da ingantaccen Irin Rogo a yankin kudu maso yamma, inda ya nemi cibiyar da ta kara fadada wannan shiri zuwa sauran kasashen da ke Nahiyar Afirka.
Tun da farko a nasa jawabin, Darakta Janar na Cibiyar IITA, Dakta Simeon Ehui, gode wa Shettima ya yi a kan shugabancinsa da kuma yadda ya mayar da hankali wajen bunkasa fannin aikin noma na kasar nan da kuma goyon bayan da yake bai wa cibiyar.

Dakta Ehui ya kara da cewa, tawagar ta zo Abuja ne; domin ganawa musamman a kan yadda za a sabunta yin hadaka da cibiyar da kuma sauran masu ruwa da tsaki, bisa nufin taimaka wa gwamnain tarayya na kokarinta wajen samar da wadatac-cen abinci a Nijeriya da kuma Nahiyar Afrika baki-daya.

Shi ma a nasa bangaren, Mataimakin Darakta Janar na IITA; Dakta Dashiell Kenton ya bayyana cewa, wannan cibiya tasu na taimaka wa wasu shirye-shiryen gwamnatin tarayya a fannin aikin noma, domin samar da damar kirkiro da wasu ayyukan yi, musamman ga matasan Nijeriya.

Haka zalika, ya yaba da fannin shirin noma don samun riba; wanda Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Tinubu ta kirkiro da shi, wanda ya yi nuni da cewa; shirin zai sake karfafa guiwar matasan kasar nan da dama.

Kazalika ya sanar da cewa, ta hanyar wannan shiri; cibiyar za ta tallafa wa manoman wannan kasa, musamman kanana ta hanyar ilimatar da su kan yadda za su bunkasa nomansu.

A nasa jawabin, Manajan Sashen Noma da Samar da Abinci na Bankin Duniya, Mista Abel Lufafa ya bayyana cewa, bankin da IITA da sauran masu hadaka; sun ji dadi da irin gudunmawar da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke bayarwa, wajen kara habaka fannin aikin noma na Nijeriya.

bankin duniya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
bankin duniya

Manoma Za Su Amfana Da Tallafin Dala 25, 000 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.