• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Ta Zargi Aliero Da Wasu Kan Yi Wa Jihar Zagon Kasa Kan Wasu Ayyuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi ta zargi Sanatoci biyu masu ci daga jihar, Adamu Aliero da kuma Sanata Dokta Yahaya Abdullahi da yi wa Majalisar Dattijai bayanai na hana bukatar da gwamnatin jihar ta yi na maida wa jihar kudaden da ta yi ayyukan wasu titunan tarayya guda biyu a kan kudi Naira Biliyan shida da Naira Miliyan dari bakwai da gwamnatocin baya suka gina a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar ayyuka da sufuri na jihar, Alhaji Abubakar Chika Ladan ne ya bayyana kan a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai kan a Birnin Kebbi, ya ce “An tafka kura-kurai da karya da ke tattare da ikirarin gwamnatin jihar na mayar da kudaden a hanyoyin tarayya, kuma sanatocin biyu sun mayar da shi tamkar wata kasuwa, in ji shi”.

  • Wata Mata Ta Shiga Hannu Kan Zargin Kashe Kishiyarta Da Tabarya A Bauchi
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 4 Sun Kwato Alburusai A Kaduna

Ya ce babu lokacin da gwamna ko wani jami’in gwamnatin jihar suka yi ikirarin gina hanyoyin biyu ba, “Duk abin da muka yi shi ne bin hakkin jihar na biyan diyya da abin da ya dace a jihar Kebbi kamar yadda aka yi wa wasu jihohi.

“Ba mu san ko wace shaida Sanata Adamu Aliero da Sanata Yahaya Abdullahi suke nema kan batun biyan jihar, shi ne ya bayar da kwangilar daya daga cikin hanyoyin biyu a lokacin da yake gwamna, shi ma ya fadi haka a zaman majalisar dattawa to mene ne hujjar shi na cewa sai mu gabatar da hujjoji aikin da muka yi. Duk takardun hujjojin da ake so suna a gaban Majalisar Dattawa da na wakilai, wacce hujja ake nema kuma”, in ji kwamishinan Abubakar Chika ladan.

Ya kara da cewa tun bayan umarnin da majalisar dattijai ta bayar na cewa jami’an gwamnatin jihar Kebbi su bayyana a gaban kwamitinta mai kula da lamuni da basussuka tare da duk wasu takardu da suka dace, domin kare ikirarin sake biya na gina titunan gwamnatin tarayya guda biyu a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Ya ce bisa ga bayanin, an gina titin tarayya guda biyu, hanya Dabai-Mahuta-Koko mai tsawon kilomita 91 a tsakanin shekarar 2006-2011 a kan kudi N5,070,912,911.47 da gwamnatin Adamu Aliero ta yi, amma gwamnatin Saidu Dakingari ta kammala shi a shekarar 2011.

Haka kuma Malando-Garin, Saidu Dakingari ne ya gina titin Baka -Ngaski-Warra mai tsawon kilomita 42 daga shekarar 2008-2013 tare da gadar mai fadin mita 90 mai tsawon mita 6 akan kudi N2,200,918,185.78.

“Lokacin da wannan gwamnati ta zo a shekarar 2015, ta gano cewa gwamnatin tarayya na mayarwa gwamnatocin jihohin kudaden da jihohin suka gina a yankinsu.

“A shekarar 2016 gwamnatin jihar ta umurci kwamishinan ayyuka na lokacin, Alhaji Atiku Bunu da ya tuntubi ma’aikatar ayyuka ta tarayya da bukaci cewa gwamnatin Abubakar Atiku Bagudu na da son a mayar da kudaden hanyoyin guda biyu da kuma wasu guda uku da suka kai Naira Biliyan 10.08.

“Sai dai ma’aikatar ayyuka ta tarayya za ta iya amincewa da hanyoyin biyu da wanda Aliero da Dakingari suka yi domin mayar da su, domin an yi su ne kafin shekarar 2015 lokacin da gwamnatin tarayya ta ba da umarnin dakatar da gina titunan gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi suka yi, an ba da izinin ne a shekarar 2020.

“Bayan haka ma’aikatar ta ba da yanke shawarar mayar da kudaden gina hanyoyin biyu zuwa Naira biliyan 6.7 kuma an ba da izinin a ranar 7 ga Satumba, 2022,” in ji shi.

Ya ce a rubuce ne jihar ta mutunta gayyatar da majalisar dokokin kasar ta yi mata domin kare ikirarinta. Ya kara da cewa, bisa wasikar da majalisun dokokin kasar biyu suka rubuta wa gwamnatin jihar, an mika dukkan takardun da suka shafi aikin gina hanyoyin zuwa ga majalisar dattawa da ta wakilai a ranar 27 ga Satumba, 2022.

“A ranar 6 ga watan Oktoba, 2022 ne majalisar dokokin kasar ta gayyaci jihar da ta bayyana gaban kwamitocin majalisun biyu, na jagoranci kwamitin mutum hudu zuwa majalisar dattawa da ta wakilai, mun samu nasarar gabatar da kararmu a gaban kwamitin majalisar wanda daga baya ya jagoranci kwamitin. Don amincewa da biyan bashin da majalisar ta yi amma majalisar dattawa ta bukaci mu jira wasu umarni amma ba mu ji su ba har muka dawo Jihar.”

Kwamishinan ya ce majalisar dattijai ta sake ba wa jami’an jihar damar bayyana a gabanta a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022, “Ya kamata a lura da cewa duk takardunmu da suka dace suna hannun kwamitin majalisar,” inji shi.

Daga karshe ya ba da tabbacin bayyana a gaban kwamitin majalisar dattijai don kare abin da kudaden da suke neman gwamnatin tarayya ta biya Jihar Kebbi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukagwamnatiGwamnatin TarayyaKebbiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Nemi Afuwar Atiku Kan Harin Da Aka Kai Wa Tawagarsa A Borno

Next Post

2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

8 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

11 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

12 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

12 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

13 hours ago
Next Post
2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya – Tinubu

2023: Ba Ni Da Kudurin Mayar Legas Birnin Tarayyar Nijeriya - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.